Kenza Novels

Kwai acikin kaya book 1

Chapter 11

All chapters

Reader mode

Kwai acikin kaya book 1 Chapter 11

4,385 words

Duk da ɓacin ran Shahudah daya fito dashi a rai, hakan bai hanashi zagewa ya maida hankali akan aikin da suke son farawa ba shi da su Aliyu abokansa. Duk suna zaune ne a cikin falon gidan da ya kaisu, Jawaad yace, "Tabbas a cikin satar kokino akwai lauje cikin naɗi, kuma tare dana kusa dashi akai hakan, bayanan dana samu yanzu haka sune, tare da amaryarsa suka dawo daga ƙasar Colonbia, kowa ya kasa gane yanda har aka sacesa babu wanda ya gani, hakanne yasakani ɗaura alamar tambaya akan wannan matar tasa, lallai tasan wani abu akai, dan a yanda tsarin saukarsa da baro airport ɗin ta kasance babu wani mahaluki dazai iya kutse wajen aikata hakan, kunsan a yanda tunanina da nazarina ya bani an sacesa?". Dukansu kai suka girgiza masa cike da mamakinsa, duk da dai dama sunsan Jay mayene akan bincike da bin ƙwanƙwanto. Murmushi yayi yana komawa jikin kujera ya kwanta, sai kuma ya tashi zaune sosai fuska a haɗe yana tsaresu da idanu, "Tabbas lokacin da aka faɗi sacesa yana cikin gidansa ne, daga baya aka fita dashi acikin gidan". "Kamarya kenan Jay? ALLAH ka sakamu a duhu, danni kam wannan case ɗin ban fahimci komaiba akansa, tayaya hakan zata kasance bayan kowa ya shaida Alhaji Kokino lafiya ya fita a jirgi, agaban kowa kuma ya shiga mota direbansa yaja shi, kuma basu tsaya ko inaba sai a cikin gidansa........." Cikin katsesa Hafiz yace, "Ni kasan mina fahimta Jabeer, kamar Jay kanason kace mana dai babu wanda ya sace Alhaji Kokino ko? Kawai matarsa tayi ƙarya da hakanne saboda wani dalilinta ko manufa ko?". Kai Jawaad ya shiga girgizawa, ya miƙe tsaye hannunsa goye duka a baya, "Fahimtata tasha banban da taku, nakula kuma irin Fahimtar da sauran jama'a sukaima abin kukeyi a yanzu, "Tabbas an sace Alhaji Kokino da gaske kamar yanda zancen ya fita duniya taji". "To waya sacesa kenan? Miyasa kuma ka kawo matarsa cikin zancen?". Aliyu daya tsare Jay da idanu ya faɗa. Murmushi Jay yayi kawai ba tare daya amsawa Aliyu tambayarsa ba, ya taka a hankali zuwa gaban Window yana leƙa harabar gidan, kusan sakwan goma kafin ya juyo gasu Jabeer da suka zuba masa idanu kamar wani magiji. "Aliyu wannan shi nake so ku fahimta nima? Ni kaina inason nasan miyasa matarsa ta shigo cikin zargina". Dukansu ajiyar zuciya suka sauke. Hafiz yace, "To yanzu dai saimu tsunduma aiki kawai, sai dai ina ganin Jay lokaci yayi da zaka yafema Rose ta dawo tare damu, kowa yasan amfaninta a cikinmu, bai kamata muyi sakaci da itaba ko a wannan lokacinma". Gaba ɗaya fara'ar fuskar Jawaad ta ɗauke, sai dai baice komaiba ya tako ya dawo wajen zamansa ya sake zama. Maimakon ya taya zancen Rose da Hafiz ya ɗakko sai ya ɗakko wani maganar daban ma. Sunsan bazai tankaba, dan wannan salonsa ne idan baya buƙatar abu, suma duk sai suka ƙyalesa kawai akan zasu cigaba da lallaɓashi har itama Rose ɗin ta dawo tare dasu su koma su biyar ɗinsu tamkar yanda suka saba a baya.....

_________________________ SHAHUDAH _________________________

Tunda Jawaad ya fice tai tsaye a wajen, bata motsaba amma ta dasama takardun daya bari manyan idanunta. A wannan yanayin Hajiya Humaira tai sallama ita da ƙanwar Shahudah ɗin mai suna Aamila.

Ko kusa bataji motsinsu ba, sai da Hajiya Humaira ta taɓata ne tai saurin juyowa a tsorace, dan tazata Jawaad ne ya dawo. Ajiyar zuciya ta sauke tana faɗawa jikin momynta ta fashe mata da kukan shagwaɓa............✍🏻

https://youtu.be/5xN4SGMIzME

Garzaya ka saurari littafin *SAUYIN ƘADDARA*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

*_ALƘALAMI TV_* ta shigo gari, tasha mai ɗunbin abubuwan ilmi, akwai littatafai na soyhayya da zasu dinga zuwa muku bisa tsaftataccen karatu, sai kuma gudunmawar hanyoyin da amarya da uwar gida zasu gyara jikinsu hankali kwance daga cikin gida basai wata taci ko sisinki ba.

Shin duk wannan gara ɓasar ka yarda ayita babu kai?🙆🏻🤔.

Maza garzaya ALƘALAMI TV dake dandalin manhajar youtobe kajiyo abubuwan bukatarka a sauƙaƙe.

Na zaune baiga gariba masoyanmu🤤🤤😋⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀⛹‍♀

A danna mana subscribing domin tabbatar da ƙaunarmu😍😍❤❤🥰🥰😘😻😻👌🏻

_ZAFAFA WRITERS: UPCOMING NOVELS: (SABON TAKU) DONT BE LEFT OUT💋❤️ CUZ YOU CANT AFFORD TO MISS THIS CHANCE🤙🏻👌🏾_

💋😍🥰😍🥰😍❤️💋

_INA GWANIN WASU GA GWANAYE NA. :INA MAKARANTA MASOYAN MARUBUTA LITTATTAFAN NA *ZAFAFA WRITERS?* NESA TAZO KUSA. SHAHARARRIN MARUBUTAN SUN SAKE DAWOWA DA KANSU BA AIKE BA. SUN SAKE ZUWA DA WASU LITTATTAFAN MASU DIMBIN DARUSSA KALA KALA. _

_RIGIJI GABJI KENAN! DOMIN DUKKANIN LITTATTAFAN NASU GUDA BIYAR DIN SUNA KAN FARASHI MAI RAHUSA WATO *NAIRA DARI BIYAR DUKA (500NAIRA)_*

_KUNGA KENAN KOWANNE LITTAFI YA TASHI A NERA DARI KACAL, KADA KU BARI A BAKU LABARI, DOMIN DA ABAKU LABARI YAFI KU BAYAR. DA NAIRA DARI BIYAR ZAKA/KI MALLAKI DUKKANIN LITTATTAFAN._

_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_

_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_

_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_

_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_

_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_

_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_

_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_

_GUDA DAYA DARI BIYU_

_GUDA BIYU DARI UKU_

_GUDA UKU DARI HUDU_

_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_

_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*

2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*

_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_

Mucigaba da shakatawa da wannan kafin a fara kafta WASAN😁👉🏻📻

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻*_Typing📲_*

*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_

*______________________________________* *_BOOK ONE_* _Shafi na sha shida_ *______________________________________*

*_Babu editing yau😔🤦🏻‍♀️_*

...........Wai nikam kukan mi kike Sister? Ni yanzufa lamarinki har mamaki yake bani, akan Brother Jawaad duk kin zama wata lusara. Hararar Aamila Hajiya Humaira tayi, hakan yasa ta ɓame bakinta. Ta mai da kallonta ga Shahudah dake kwance a kafaɗarta, "Babie na tashi muyi magana". Tashi Shuhudah tayi zaune, Hajiya Humaira tace, "miya sakaki kuka?". Cikin tsagwaron taɓara Shahudah ta fara magana da shashshekar kuka, "Momy wai ni yau Bb yake iya cewa na zaɓi ciki koshi? Harni yake iya furtama zai saki akan cikin da bai gama zama mutumba ma, dama ashe baya sona ban saniba...." Ta rushe da kuka tana faɗawa jikinta. Hajiya Humaira tai murmushi tana buga bayan Shahudah, "Ba sonkine bayayiba Shahudah, wannan abun daya ambata miki ma shine ya nuna yana tsananin sonki, duk wanda yake son haɗa jini da kai aikuwa yana sonka Shahudah". Shahudah ta ɗago da sauri baki a kumbure, "Wlhy Momy baya sona, tunda har bazaiso abinda nake soba, ni gaskiya ban shirya haihuwa yanzuba, salon nazo na tsufa yaje yana kallon wasu a waje ko?". Dariya Aamilah ta kwashe dashi tana faɗin, "Tab ashe su wata ta kusa komawa jagwal, na rantse karma ki yarda, toke ta yaya kikai sake ciki ya shiga jikinki ma?". "Zanci ubanki Aamila, tashi kibar ɗakinnan" Hajiya Humaira ce tai maganar a zafafe. Hakan yasa Aamila tashi ta fita tana ƙunƙuni da buga ƙafa na rahin samun isashshiyar tarbiyya. "Mamana karki biyema Aamila kinji, ki kwantar da hankalinki akan wannan cikin tunda yazo a kuskure, koshi kaɗai kika haifa ya isa haka, zuwa nan gaban idan kinso saiki ƙara ɗin, kinsan dai Jawaad yanada Zuciya idan aka ƙure haƙurinsa, kaɗan daga aikinsa ya aikata dukkan abinda ya faɗa, kuma Abbanku ma yaji faɗa zai miki, insha ALLAH haihuwar wannan cikin sai dai ya ƙara miki daraja a wajen Jawaad badai ya rage mikiba, ALLAH yasa ki haifa mana little Jawaad dai mu shine babban fatanmu". Shahudah dai da maganar bata gama shigarta ba tace, "Yanzu kowa dai baya sona a gidannan, ni wlhy barmuku ƙasar zanyi to, dama saboda shi na dawo cikinta, tunda ya fara wulaƙantani gara nai gaba abuna". "Kefa wata sa'in baki da man kai Shahudah, lokacin da ake nuna miki Annabi saiki ta ƙoƙarin rimtse idonki haba, banason shashanci mana, to wlhy ki tabbata inhar kika zuba da cikinnan ba Jawaad kaɗaiba hatta ni da Abbanku mantawa zamuyi dake shasha kawai mai girman banza". Yanda Hajiya Humaira ta fusata sai abun ya bama Shahudah mamaki, hakane yasaka ta tsura mata ido kawai, miyasa kowa kejin haushinta akan wannan cikin? Tana kallo Hajiya Humaira ta fice ta barta, kwanciya tai ta rushe da kuka, sai da tayi mai isarta sannan dabarar kiran Qaseem tazo mata. Bugu ɗaya kuwa ya ɗaga, cikin kuka ta sanar masa da duk abinda ke faruwa. Da farko shima kamar zai mata masifa akan zubda cikin sai kuma yay saurin haɗiyewa ya kwantar da murya. "Haba Shahudah na, manta kawai da batunsu, koni banso kika ɗauki ciki yanzuba, amma kuma yaya muka iya, ni badan ina tsoron akan ance idan mata sukaje zubda ciki suna mutuwa ba da dakainama zan kaiki a zubar dashi gaskiya". "Broth da gaske wai ana mutuwar dan ALLAH?". "Da gaskene fa Dear". "Tab wlhy banson na mutu, amma kuma ai itama haihuwar wlhy ance ana mutuwa". "Eh amma ai kinga bakamar idan za'a zubar da cikiba, ki kwantar da hankalinki kawai kinji Sweetsister, ke dai kawai kina haihuwar wannan ki ɗauki mataki kinji". Haka yayta lallaɓata da kalamai masu sanyi harta aminta da zancensa. Bayan sun ajiye wayar yay ƙwafa, wlhy badan shima yana da buri akan cikinnan na jikin Shahudah ba da sai ya sakata zubdawa koda ya baƙanta ran Jawaad, dan yasan zubda cikinnan ba ƙaramin sukar zuciyarsa zaiyiba, amma babu komai, idan yasha a wannan ai bazai sha ba anan gaba.

Itakam Shahudah shawarar Qaseem ce ta sakata yarda zata bar ciki, amma wlhy saita rama wulaƙancin da duk Jawaad yay mata a gidannan, bazata sake ɗaga masa ƙafaba daga yanzu....

_______________________ BILKEESU _______________________

Gidan nasu bawani mai ƙyau bane, ginine dai irin na masu ƙaramin ƙarfi, darene shiyyasa bazan iya ƙarar da komai ba dan gane da tsarinsa, gashi anguwar babu wuta. Mun shiga da sallama bayan ya ajiye napep ɗinsa inda yakan ajiyeta, gidan shiru kamar babu kowa, sai muryar mutum ɗaya da najiyo ta amsa, ta fito tana ƙoƙarin ɗaura zaninta, amma ganinmu sai ta tsay turus tana haɗe fuska. "Wannan fa?" ta faɗa muryar ta na ɗaukar zafi. Ina jinsa yay gajeren tsaki, kamar bazai bata amsaba sai kuma naji yace, "Inna tai barcine?". "Ni ban saniba" tai maganar tana juyawa fuska a kumbure. Kansa kawai ya girgiza ya nufi ɗakin dake can wani ɗan lungu yana min nuni dana biyosa. Munyi sallama amma ba'a amsaba, ya ƙarasa shiga ɗakin nima ina biye dashi a baya. "Inna harkun kwantane?" Tsohuwar dake kwance mai tsananin kamanni da Innata ta ɗaga masa hannu cikin yanayin barci tana faɗin, "Uhm, ka dawo da wuri haka?". "Eh wlhy inna, amma ina tare da baƙuwane". Babu shiri ta tashi zaune, takai hannu ta ƙara hasken fitilar dake ajiye saitin fuskarta ɗakin yay fayau. "Aibo baƙuwa daga ina kuma a tsohon darenan?". Sai da gabana ya faɗi dajin furucinta, amma amsar da naji ɗan nata na bata ce ta sakani sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya. "Inna zan miki bayani da safe, yanzu dai gata nan bara na samo mata abinci wajen Lawusa". Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, ta kalleni fuska babu walwala tana min nuni da wajen zama, zama nayi jikina duk a sanyaye, dan banga alamun zan samu karɓuwa ananba kam. Muna zaune shiru kaina a ƙasa saiga Shu'aibu ya dawo ɗauke kula, a gabana ya ajiye yana faɗin, "ƙanwata maza kici saiki samu ki kwanta kinji". Godiya nai masa, na buɗe kular dan yunwa nakeji, Taliya da wakene a ciki, ban cutama kainaba naci na ƙoshi, dan rabon da na samu nutsuwar cin abinci haka tun ranada zan buge Jazuga. Tabarma Inna ta bani, na shimfiɗa inda nake zaune na kwanta, filoma sai da ledar da Sani ya bani wadda bansan ko minene a cikina nai filo, kafin kace kwabo barci mai nauyi yay awon gaba dani. Ban sake sanin halin da ake cikiba sai da asuba da inna ta tasheni nayi sallah. Ina daga inda nai sallar ne na gaisheta. Ta amsa min cikin halin ko in kula ta fice abinta, lallai nasan akwai matsala, a yanzuma batasan koni wacce ba ban damu karɓa daga gareta ba inaga ta ji wacece ni?. Haka na zabga tagumi ina komawa duniyar tunanin yanda rayuwa take tamkar juyawar ƙarfunan agogo, wani lokacin sai kaga komanka nata maimaici bisa ga matsalolin rayuwa, idan kai wasa tuni kake aikata saɓo koda afurucine. Shigowa inna da Shu'aibu ta katse mani tunani, na gaida shi bayan sun zauna. Cike da fara a ya amsa yana tambaya ta ya baƙunta?. Nai ɗan murmushi mai sauti ba tare dana iya cewa komaiba. Hankalinsa ya maida ga inna daketa faman taɓe baki tana kallonmu, "Inna kinsan wacece kuwa wannan?". "Yazan sani baka faɗaba Aibo". Ƴar dariya yayi yana gyara zama, yace, "Kalleta da ƙyau dawa tai miki kama?". Kallona Inna tayi, sai kuma taɗan taɓe baki, "Yo kai banda abinka Aibo ina nake ganin fuskarta, tunda ta shigo gidannan banda sinne kai da take kamar sabuwar amarya mi takeyi". Saurin ɗago kaina nai na kalleta, sai dai kuma ban jureba na janye idanuna, amma dai nasan yanzu zataga fuskar tawa kamar yanda take buƙata. Inajin yanda idanunta ke yawo a jikina, zuwa wasu mintuna kamar biyu tace, "Ina gano kamannin Zubairu da Asiya tare da ita kuwa Aibo". Dandanan bakin Shu'aibu ya washe, cike da zumuɗi yace, "Masha ALLAH, ai ɗiyar Inna Asiyar ce kuwa inna". "Ɗiyar Asiya? Kai ina ka samota haka?" Inna ta faɗa cike da mamaki. Murmushinsa ya faɗaɗa, tas a yanda muka haɗu jiya sai ya sanar mata, sai jinjina kan mamaki takeyi, ta juyo gareni tana tambayata daga ina nake haka har shi Shu'aibu ya ganoni?. Da farko nayi niyyar faɗa musu gaskiya, amma yanayin Inna da naga har sannan bawani ɗokin ganina taiba saina canja zancena kawai, na faɗa musu iya abinda zasu iya amsata game da nemnsu kawai na fitoyi dan nagaji da zama ni kaɗai. Kai inna ta jinjina, babu ko jin nauyina tace, "Amma kai Aibo kana ganin riƙon babbar budurwa kamar wannan bazai zamar mana wani tawayaba? Mu dai ba kuɗin aurar da ita ke garemu ba kaima kasan haka, ga ɗan karen kishin matarka da batason ganin wata mace ta raɓeka, inaga mu taimaka mata da wani abun ta koma inda ta fito tai haƙuri kamar yanda kowa keyi a nasa gida. Murmushi nayi mai ciwo hawaye na taruwa cikin idona, wato sai yanzu na fahimci abinda yasa dangina ke gudun ɗaukata, ashe hidimar aurar danice damuwarsu kawai, to nida banida ko saurayi wane maganar aurena za'ayi kuma?, maganar shu'aibu ta katseni. "Haba inna, wannan wace irin maganace haka, koba komai ai Bilkisu abar tausayice, ALLAH kuma shine zai buɗa mana mu sauke dukkan nauyinta gwargwadon iko, dan riƙe maraya ba ƙaramin alkairi bane da falala ga bawa, amma yanzu sai kowa ke gudun hakan, kifa tuna mahaifinku ɗaya da inna Asiya, na tabbata kuma da itace a raye zata riƙe naku ƴaƴan ai, sa......" "Nikam naji gwanin iya magana, tunda kaji ka gani ta zauna ga fili nan, ni dama dai kai nake tausayi, tunda dukkan ƙarfin riƙe gidannan kaine keyi". Cikin jin daɗi yace, "Nagode da amincewarki inna, ALLAH ya tayamu riƙo".

Wannan shine yazama sanadin zqmana a wannan gida, duk da bajin daɗin zaman nakeba hakan ya fiyemin akan naje naita raɓe-raɓe harna cigaba da gamo da irin gidajen su Uwargida masu dulmiyar da imanin bawa zuwa halaka. Babu mai sakarmin fuska inba Shu'aibu ba, shi kuma ba yini yake a gidanba, a hankali dukkan aikin gidan ya dawo kaina, sam bani da wani hutu inba dareba shima sai kowa ya rigani kwanciya. Lawusa matar Shu'aibu ta mugun tsanata, ni zan dafa abincin gidan amma idan tazo rabo ɗan kaɗan take zubamin, wani lokacinma saita gama rabon zatace ta manta dani, sai dai ace na kankare ƙanzon. Duk da agaban Inna ake komai uffan bata ce mana balle ta nunama Lawusa batai dai-daiba, koda yake na lura Inna tsoron Lawusa takeyi, dan haka zatai ta mata rashin kunya amma bata iya cewa batai dai-daiba, sai idan taimata abinda yay mata zafine sosai zakaji ta faɗama Shu'aibu, shiko iyakarsa yace tayi haƙuri ta bar Lawusar da halinta kawai. Wannan zama nasu na bani mamaki sosai. Ban fahimci abinda yasa gidan yake hakaba sai da ƙanwar yaya Shu'aibu Sa'a tazo gidan yini a ranar da nake cika wata guda a cikinsa, itakam hannu biyu ta amsheni, sai murna take matsayina na ƴar uwarta. Akan Lawusa namin masifa nazo na ɗaura abincin rana sukai faɗa da Sa'a, tace ban ɗorawa ita da take aure a gidan ta fito ta ɗaura, da yake Inna batanan sai babu wanda yace Sa'a batai dai-daiba, nicema naita bama sa'a haƙuri akan tabari kawai nayi, amma fir tace bazanyiba. Nanne ta zauna ta bani labarin ai Yaya Shu'aibu ba son Lawusa yakeba, Inna ce ta haɗa auren saboda Lawusa ƴar ƙawartace, yanada wadda yakeso amma inna tace bazai aureta ba sai Lawusa. A lokacin babansu na jiyya baida lafiya, shiyyasa aka rasa mai goyama Shu'aibu baya, dole ya auri Lawusa badan ya soba, bayan bikin da sati biyu kuma babansu yarasu, daga nan Lawusa ta fara ma Inna rashin mutunci a gidan, inna ko bata iya ce mata komai, yanzu haka aurensu shekara uku kenan, amma ko ɓari Lawusar bata taɓa yiba sai rashin mutunci, sai dai duk wannan tijara tata tana tsoron Shu'aibu, ita kuma Sa'a bata raga matane. "ALLAH ya ƙyauta" kawai na iya faɗa naja bakina na tsuke. Sai yamma lis Inna ta dawo gidan, Lawusa ta kwashe ƙarya da gaskiya ta faɗa mata a kaina, Inna ko ta rufeni da masifa hardasu gori akan daga taimakona da sukai shine zanzo na watsa musu gida. Ran Sa'a ya ɓaci akan wannan abu, Shu'aibu na dawo ta kwashe komai itama ta sanar masa, shiko ya balbale Lawusa da masifa har takaisu ga marinta. Kuka da ihu taita kurmawa akan mari guda ɗaya, yayinda bakinta keta danƙarama Shu'aibu zagi ta uwa ta uba, ta haɗa kaya zata tafi Inna taita roƙonta da bata haƙuri, sai da ƙyar Lawusan ta haƙura saboda tana bala'in son Shu'aibu, batason rabuwa dashi sam. Ni daga baya ma abin nasu dariya ya koma bani dan na lura dama Lawusa bason tafiya takeba, farfaganda ce kawai. Sam abinda akemin a gidan sai baya damuna sosai, komai kuma suka buƙata ina musu dan a zauna lafiya, ban taɓa ɗaga kai na kalli wulaƙancin da Lawusar kemainba sam, a ganina ba laifinta bane ai, haka ƙaddarar rayuwata take.....

________________________ JAWAAD _________________________

Yau ma dai Jawaad bai kwana gidanba, koda ya baro wajensu Aliyu Office ya koma, acan ya raba dare yana aiki, daga baya ya fito, amma saima ya rasa ina zai dosa, sam baya buƙatar komawa gida, dan bayason yawan ɓacin rai a yanzu, yana buƙatar nutsuwa ta musamman akan gudanar da wannan aikin da yake fatan nanda kwana biyu ya kammala shi insha ALLAHU.

Gidan dasu Jabeer suke dai ya sake komawa, ya iske har sunyi barci, dan haka ya buɗe wani ɗakin ya shiga ya kwanta, bama wani barci sosai yayiba aka kira asubahi. Su Hafiz duk sunyi mamakin ganinsa a gidan, sai dai tunda bai basu fuskar da zasu tambayesa komaiba sai basuce ɗinba. Suna dawowa daga salla duk da barcin dake cin idonsa bai kwantaba. Zama sukai yana musu bayanin abinda kowa ya kamata yayi a ranar yau.

Coffee da Jabeer ya dafa musu da kansa kowa yake sha, Jawaad ya ajiye kofin hannunsa yana faɗin, "Dolene yau muyi komai da azama, dan guri na sake ƙure mana. Ni zanje gidan Alhaji kokino na gana da matarsa, Jabeer kaikuma filin jirgi ya kamata kaje ka sake mana bincike a cctv ɗinsu, Aliyu da Hafiz ku kamo mana drivern Alhaji Kokino da ƙaninsa wakili, dan hardashi akaje tarbosa filin jirgi, shima inada alamar tambaya a kansa". A tare duk suka jinjina masa kai, sai kuma kowa ya miƙe domin zuwa ya shirya...............✍🏻

https://youtu.be/5xN4SGMIzME

*_ALƘALAMI TV_* takuce, maza ku garzaya kar ayi babu ku, Please a danna mana subscribing domin nuna mana ƙauna ta musamman🥰🤙🏻.

🗣 *_RANAR KUKE JIRA YAU GATA TAZO📻📻💃🏻💃🏻💃🏻_*

*_ZAFAFA 👭🕴🏻👫, DA TAMBURANMU GAMU MUNZO💃🏻💃🏻💃🏻📻📻_*

*_MASOYA MUKE KIRA DAN KUWA MUNZO💃🏻💃🏻🤫😉😂_*

*_Dan dan dan dan dan, ina masoyan suke?, ga fa ZAFAFAN BIYAR sun sake faso muki da wani SABON KAFCE mai tsuma zuciyar abokin tafiya_*

_ZAFAFAN dai nan nakune, waɗanda suka barbaje basirarsu a littatafai biyar da suka shuɗe, masu saka nishaɗi da tada kunnuwan mai karatu sama tamkar yana tailunar kilishi😉_.

*_Kunsan wanima abin jin daɗi kuwa? To wlhy ina mai tabbatar muku KAFCEN wannan lokacin ya ɗara na farko, domin kuwa madarar basira zasu kwarayar, tare da nagartaccen ilimi mai garɗin dabino_*

_Maza ku garzayo dan kaɗan ya rage a fara al'amura, farar takarda da biriknmu duk riƙe suke a hannu, hallaruwarku guri gudane zai bamu ƙwarin gwiwar suburbuɗo muku daɗaɗan labaranmu kamar haka._👇🏼

_*IGIYAR ZATO.....*:- Na marubuciya Hafsat (miss xoxo), labarin soyayya mai ƙyatarwa, cakuɗe da tsagwaron cakwakiyar ruguntsumin abin al'ajabi_.

_*ƘAUNAR MU:-* Na Mamu gee, labarin madarar soyayya ƴar asali da babu sirkin ruwa a cikinta, ga wata sambaɗeɗiyar zumar zaƙin daɗi mai saka zuciya zumuɗi._

_*ƊAURIN GORO...:-* Na Hafsat rano, Kitumurmura kenan, amma ta lobayyar baje basirar ƙofofin zukatan masoyan da suka samu ɗaurewa bisa makirci ta cakwakiyar maƙiya_

_*ALƘAWARIN ALLAH:-* Na Safiyya huguma, labari mai tsagwaron nuna jarumtar masoyan da ƙaunar gaskiya ke ambaliya da dulmiya cikin tsantsar ƙauna, dukda ɗunbin zagon ƙasar da ake tafka musu._

_*GUDU DA WAIWAYE....:-* shi ya kawo mugun zato. inji masu iya maga. Na Bilyn Abdull, labari mai ɗaure da sarƙaƙiya a zukatan masoyan da yarda ta amince musu kasancewa a inuwa ɗaya, amma tsagwaron cakwakiya da hargitse-hargitsen ƙaddariri suka tarwatsa hakan._

*_Tabɗi jan, wannanfa shine ZAFAFAN, to kai mai karatu tayaya zaka tabbatar zafafanne?, bari na baka satar amsa😁👇🏼_*

_*Amsar itace😉*👉🏻 ƙoƙarin mallakar ZAFAFA ta tsafta tacciyar hanyar sanƙamawa jagororin tafiyar kuɗi kamar haka.👇🏼_.

_*NAIRA 500*, mabuɗin mallakar litattafan ne gaba ɗaya biyar hankalinka kwance_

_*NAIRA 450*, Zata mallaka maka littatafai huɗu._

_*NAIRA 400*, tikitin mallakar littatafai uku_.

_*NAIRA 300*, zai baka lasisin mallakar littatafai biyu_.

_*NAIRA 200*, Na mallakar littafi guda ɗayana._

*_Kunji wata rahusa ƴan uwa? Yo duk saukinnan saiki zauna daɗaɗan labarannan guda biyar su wuceki duk da gwanayenki ne mamallakansu?🤔😳_*.

_Maza garzaya ki sanƙama ƴan kwabbanki ta wannan asusun bankin domin mallakar zafafa masu sanyaya zuciyar mai karatu._

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*

2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*

_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_

Mucigaba da shakatawa da wannan kafin a fara kafta WASAN😁👉🏻📻

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻g*_Typing📲_*

*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_

*______________________________________* *_BOOK ONE_* _Shafi na goma sha takwas_ *______________________________________*

*_Babu editing yauma😂⛹‍♀_*

...........A mamakin kowa sai mukaji Inna tace, "To kukam ALLAH ya ƙyauta muku, na lura sam jininku bai haɗuba, bara Aibo yazo, ai na samo maganin wannan yawan fitinar taku mara dalili". Ba Lawusa kawaiba, koni kaina nayi mamakin maganar inna, danni a zatonama yau saita koreni a gidan saboda na taɓo ƴar mai ɗinta, amma ji yanda ta nunama halin ko in kula akan zancen, sai daimaganarta na ƙarshe akan mafitar data samo ta tsayan a zuciya sosai, komawa nai na kwanta ina rawar sanyina. Lawusa kam kuka ta sanya rurus wai dama inna bata ƙaunarta ai a gidan, yau sai ta tattara ta barmusu gidansu, sai inna ta aurama Sha'aibu ni a yau da rana danta nuna ma duniya ni ƴar uwartace". Duk surutan nata dai inna bata kulaba, matan kuma da sukazo haɗa munafinci sai gasu suna jan ƙafa suna fita ɗai-ɗai da kunya. Ina jiyo fitar Lawusa tana cigaba da zagin Inna. Kaina kawai na girgiza ina mamakin irin wannan tarbiyya ta Lawusa, a hakane wannan zata zama uwar wasu, ita kanta tana buƙatar tarbiyyar balle abinda zata haifa. A haka wahallalen barci ya kwasheni, ban tashi farkawaba sai lokacin sallar zuhur, shima dai inna ce ta tasheni akan naje nai sallah. A mamakina kuma na fito zanyi alwala sai naga inna tayi abincin rana da kanta bata tasheni ba. Salla nayi, ina zaune sai ga sallamar Yaya Shu'aibu ya dawo cin abincin rana kamar yanda ya saba, muryar Inna na tsinkayo tana sanar masa bani da lafiya, hakan ya sakashi faɗin "Subahanallahi, miya sameta kuma?" yay maganar yana ɗage labulen ɗakin. Sannu nai masa sannan na gaishesa, cike da kulawa ya amsa, ya ƙarasa shigowa ɗakin yana tambayata mike damuna?. "Yaya zazzaɓine kawai, kuma Alhmdllh yama sauka". "Wayyo sannu, ai ko sauron gidannan ya isa saka mutum zazzaɓi, kici abinci saina kaiki kamiz ki amshi magani". Nace "to" tare da masa godiya. Nanma nazata Inna zatace a'a sai naji batace komaiba, sai ma amsar tambayarsa akan Lawusa take bashi, duk abinda ya faru tsakanina da Lawusar ta zano masa, ta ɗora da faɗin, "Ni yanzu na samo mafita akan wannan yawan rigimar tasu, fitar danai yau wani gida ƴar kande ta rakani na samowa Bilkisu aikin wanke-wanke da shara, inasha ALLAHU tananma sai kaga ta haɗa kuiɗin kayan ɗakinta har muma mu mora, kaga bama ta yini gidanba balle wannan fitinar ta cigaba da girmama a gidannan". Shu'aibu da fuskarsa ta ɗan nuna alamun damuwa, yace, "Amma Inna ni dai da kinyi shawara dani da ba'ayi hakaba, wane kuma aikin wanke-wanke Bilkisu zatajeyi fisabillahi, ni dai duk da sana'ata ba wata mai ƙwari bace zanyi iya bakin ƙoƙari wajen sauke haƙƙin zuminci akan komai na aurenta, indai dan zaman gidane zanma matarcan ta tsallake magana Bilkisun taje ta fara koyon ɗinkin jakka a wajenta, kinga ko aure tayi ai tasamu madogara insha ALLAHU". Ran inna a ɓace tace, "Nikam Aibo bansan miyasa kake nina tamkar ina zalintar yarinyarnanba, yanzu shi aikin da zataje bazai taimaketaba ne? Ko aure tayi ai dai ta samu ta iya komai". "Hakane Inna, nima banƙi ta takiba, muyi addu'a to ALLAH ya zaɓa abinda yafi alkairi a ciki, idan ta samu lafiya sai muyi maganar". "Shike nan" Inna ta faɗa a taƙaice, da alama dai har yanzu ranta babu daɗi akan canja mata tsari da yayi.