Kenza Novels

Kwai acikin kaya book 1

Chapter 20

All chapters

Reader mode

Kwai acikin kaya book 1 Chapter 20

4,080 words

Tun a harabar gidan nake tsarkake sunan ALLAH, dolene akira dukiya jarabawa ga bawa, yanzu mai wannan muhallinma dan yace ya manta da danginsa ai bakaga laifinsa ba, wani dai saikaga tamkar alƙalamin rubuta ƙaddarar rayuwarsa a hannunsa yazo....... Zungurata da akaine ya sakani dawowa hayyacina babu shiri, harara ta gallamin da jan tsaki, "K dalla baƙauyar banza ki wuce muje, kin wani zauna kallon gida, halan yau kika fara ganin irinsa?". Bance komai ba, sai bin bayanta da nayi kawai. A falonma dai akwai abin kallo da bakima bazai iya lissafowaba, abinda kawai zan iya faɗa hotunan masu gidan da aka ƙawata adon falon dasu, a yanda naga hotunan da alama yaran nasama sun zarta biyu, dan kuwa bayan waɗan na gani ga mutane uku kuma a hoto, namiji haɗaɗɗen saurayi maiji da kansa, sai ƙyaƙyƙyawar budurwa da tafi dukkan ƴan gidan asalin ƙyawu, saikace wata jinin larabawa, dan nikam bazan ce baturiya ba, dan ba ƙyawunsu nake ganiba, sai dai shigar tatace kam sak ta turawan ce, sai hoton namiji again da bazai wuce shekaru goma sha biyarba, hoton dai da gani tsohon hotone. Na sake waigawa ko zanga inda yake babba sai dai babu. Tunda muka shigo kawu saman bene ya haye, hakan ya saka hajiya binsa itama. Suma duk sai suka shige ɗakunansu aka barni ni kaɗai a falon tamkar mayya, hakan baisa naji rashin daɗiba, koba komai nasamu damar yima falon kallon tsaf ai.

Sakkowar hajiya daga saman bene ranta a ɓace ne ya sakani kallonta, sai kuma na duƙar da kaina saboda mugun kallon data jefeni dashi, kafin tace wani abu sai ga Kawu ma ya sakko fuskarsa babu walwala. Ni dai dama a ƙasa nake zaune, sai na ƙara ladabtuwa domin girmamawa a garesu. Kawu yace, "Ɗiyata taso muje kiga ɗakinki kinji". Cikin girmamawa na amsa da "to" ina miƙewa, yana gaba ina biye har ɗan lungun dake falon, ɗakuna ne a jere guda biyu, muka isa har gaban na ƙarshen ya buɗe ya shiga, nima shigar dai nayi. Ɗakine babba sosai, akwai komai a ciki na amfani tamkar ɗakin matar aure, matar aurenma ƴar gata ta gaske. Da ƴar ƙura a cikinsa kaɗan, alamun dai ba amfani ake dashiba, komai na ciki kuwa kalar ja da fari ne....... "Bilkisu nan ne zai zama ɗakin ki kinji, shi ɗin ɗakin ƴar uwarkice datai aure kusan wata tara kenan, yanzu kinga saiki maye gurbinta, inason ki kwantar da hankalinki a gidan nan, ki ɗauki kanki tamkar kowa na cikinsa, yanzu dai idan kin huta zuwa dare zamu zauna dan ki san kowa da sunansa kinji". "To kawu nagode sosai, ALLAH ya ƙara buɗi da haske na alkairi". Fuskarsa faɗaɗe da murmushi yace, "Amin ɗiyata, amma daga yau ba kawu ba, ki kirani Dad kamar yanda ƴan uwanki suke kirana dashi, kema yanzu baki da banbanci dasu a gareni kinji". kaina na ɗaga masa nima ina murmushin jin daɗin dajin tsantsar ƙaunarsa a raina, shine mutum na shida da arayuwa bazan manta da suba, domin sunji tausayina a lokacin da nake buƙatar hakan ga kowa, sun ƙyautata mani lokacin da jama'ar duniya suke guduna, na share hawayen da suka ziraromin a fuska. Jinai kawai an kama hannuna, na ɗago na kallesa aɗan firgice, "Haba ɗiyata, banason na sake ganin waɗannan hawayen a fuskarki dan ALLAH, nasan bazan iya ɗauke miki dukkan matsalarki ba a rayuwa, amma insha ALLAHU zan kamanta kinji, ki daure ki saki jikinki, zanji daɗin hakan". Murmushi nai masa, "Insha ALLAHU Dad bazaka sake ganiba". "To Alhmdllh ƴar gidan dad" yay maganar yana rungumeni. Duk saina rikice, miye hakan kuma kawun yay min?, nashiga ukuna. Shima fuskantar abun yazomin wani iri ya sakashi sakina yana faɗin, "muje na nuna miki yanda zaki amfani da banɗaki".

Komai sai da ya nuna min shi, yakuma tabbatar na fahimta sannan ya fita ya barni ina ƙara gwada fahimtar komai yanda bazan manta ba. Daga baya kuma na zage na gyara ɗakin tsaf, sai naga ya sake ƙyau saboda gyara na musamman daya samu sosai.

★★★★★★★★

A daren ranar wajen cin abinci na sake sanin kowa na gidan, dan kuwa duk Dad yaymin bayani a kansu da sunansu. Duk na fahimta, duk da dai na kula shi kaɗaine ke ra'ayin zamana a gidan, dan ko babban ɗansu da alama ban cikin tsarinsa shima, sai kallon ƙurilla yake bina dashi a yatsine, wanda hakan ya tunomin da Jazuga a zuciyata, koda na koma ɗaki sai da na zubda hawaye saboda tuno firdausi da su inna da nayi, ina kewarsu sosai, inason sanin halin da suke ciki kuma. Naci kuka a wannan daren har na rasa hawayen tsiyayarwa, dukkannin komaina na baya ya shiga dawomin daki-daki, ganin ina neman cinye daren da tunani sai na tashi na ɗauro alwala nazo naita nafilfilina ina miƙama ALLAH godiya da kukana game da sabuwar rayuwar dana sake shigowa.

Tabbas rayuwar wannan gida tasha banban da duk inda na rayu, ba'a ɓangaren jindaɗiba kawai harda yanayin zamantakewa da tarbiyya. Gashi dai ina samun komai na buƙata, dan ko sutura kwana na ɗaya a gidan dad ya kawomin masu yawa, sai dai kumafa duk ƙananune, dan babu ko ƙyallen atanfa. Abincin da kowa zaici nima shi nakeci, babu wani banbanci tanan ɓangarenma. Sannan bana aikin komai a gidan, kamar yanda yaran gidan suma basa komai sai ƴan aiki, ko gyaran ɗakina ma sai da nai magana mai aikin gidan ta daina min. Yanayin tarbiyyar gidan ce dai sai addu'a, dan kuwa na kula dai tsantsar rayuwar turaice da ɗabi'unsu ke wanzuwa ga jama'ar gidan. Duk kayan daga gadama zaka saka babu ruwan wani da kai, babu mai maka faɗan rashin dacewarsu, rungumar juna tsakanin mazan da matan hakan ba komai bane, shima Dad ɗin dazai tsawatar rungumemu yake, rashin girmama na gaba matsayin na yayanka wannan sam babu shi, ɓangaren ibada ba damunsu tayiba idan har ka cire Dad da ba kullum yake zama gidanba, bazan ce maka arana suna cika salla biyar babu tsallake ba har Mommy ɗin, maganar Qur'an ma ban gansa a gidanba tunda na shigo, amma akwai ɗaki na musamman domin karatu, cike yake da kowanne nau'in littafin daya shafi boko harma dana labaran turanci, komai kayi a gidan sunansa ƴanci kawai, babu mai cemaka akwai kuskure a ciki.

Duk ɗabi'un nasu sunmin girma, na kasa kwaikwayon ko guda ɗaya a ciki balle na riƙesa matsayin cigaba. Hakan yasa a kullum suke hantarata da suna baƙauya ko bagidajiya, bana damuwa dan bana samun sakewar fuska daga kowannensu dama idan ka cire Dad, idan baya gida babu maimun magana sai hantara da harara. Iyakar nan dai tsananin ya tsaya min, shiyyasa bai cika damuna ba sosai. A ƴan kwanakin dana samu a gidan jikina harya fara nuna alamun canji, dan kuwa fatata ta fara gogewa, sannan jikinma dai da alama ƙiba zai fara, baƙina da kullum suke zagina a kansa ya fara korewa, dan duk sanda Yah Qaseem zai hantareni yakan kirani da suna baƙar banza. A kwai ranarda Yah Salman ke faɗin wai dama na taimaki kaina nazo ya kaini asibiti anmin allurar da zan koma fara ko nayi ƙyan gani, danshi wlhy har kunya yakeji suzo suyi baƙi aga ɓaƙar fuskata a cikinsu, ni da kwalta ta titi bamu da maraba. Dariya Aamila da Mummy sukaita tuntsurawa akan wannan zance, harma Mummy ke faɗin, "karka damu, sonake mu fita shopping ai na haɗo mata mayukan da zata kore wannan mugun baƙin, ni kaina baƙin nan nata har tayarmin da tsigar jikina yakeyi, anya Bilkisu nama taɓa ganin mai baƙinki kuwa?". Murmushi kawai nayi ina haɗiye kukan da yake shirin taho mani. Yah Qaseem yaja tsaki shima daga inda yake zaune yana cewa, "Ku baƙin kawai kuke gani, ni wlhy nafi tsanar naniƙaƙƙen hancin yarinyarnan, sai kace tana gudu aka saka mata, wannan ko farin tayi an faɗa muku fasali zatayi? Indama ALLAH ya sota ya bata jiki mai ƙyau, gashi dan jaraba kullum tana fama da wannan hijjabin sai kace akanta aka fara addini, idanma zaki sauƙaƙama kanki ki sauƙaƙa yarinya, larabawanma tushen musuluncin sha'aninsu sukesha balle ke jinin wahala". Nan ɗinma dariyar sukayi, hakan ya sakani kasa jurewa sai da yawayen da nake riƙewa dai suka zubo, hijjab na saka na share kawai. "Tofa, wai kuka kikeyi dan an faɗa miki gaskiya? Tab kinada aiki wlhy" Yah Salman ne mai maganar yana miƙewa zai fice. Haka suka cigaba da cimin fuska kowa na faɗin albarkacin bakinsa, dawowar Dad ce ta ceceni na samu sukuni, shikuma ganin yanayina ya sakashi tsareni da tambayar lafiya?. Nace masa babu komai daga barci na tashi

★★★★

Ina sati na huɗu a gidan da safe kowa ya fice, daga ni sai Aunty Aamila da mummy ne a gidan, kuma duk suna ɗakunansu suna barci, niko bana iya dogon barcin nan hakan ya sakani fitowa falo na zauna ina kallo a tv, ɗauke wutar da sukaine ya saka ni miƙewa, ga shirin gidan kuma yasaka naji duk kaɗaici ya taso mani, tashi nai na koma ɗaki na kwanta duk da nasan ba barcin zanyiba.

★★★★

Da ƙyar Shahudah ta iya isa gidansu saboda rashin jin ƙarfin jikinta, tai hon mai gadi ya buɗe mata, yana ma gaisheta amma bata sauraresa ba ta shige, koda tai fakin ma kanta ta kwantar a sitiyari tai shiru na wani lokaci, kusan mintunanta biyar sannan ta samu ta fito zuwa cikin gidan. Yanda gidan yake shiru tasan su mummy basu tashi barciba, gashi tana buƙatar hutawa, tsohon ɗakinta ta wuce danta samu ta hutama ranta, dama inhar tazo gidan takan zauna acannane.

Takun takalman da najine ya sakani kallon ƙofa, har aka buɗe aka shigo. Idanuna suka saukakan ƙyaƙyƙyawar matashiyar mace cikin ado na ainahin zubin wayewa ta shigo ɗakin babu ko sallama. Tozali dani ya sakata zare baƙin glasess ɗin idonta da ya rufe kusan rabin fuskarta tana min kallon sama da ƙasa, nason sanin ke kuma wacece haka?. Nikuma cire glasess ɗin natane ya bani damar ganeta duk da a hoto na taɓa ganinta, ɗiyarsu Dad da aka bani ɗakintace mai suna Shahudah kamar yanda ya sanarmin ce, yauce ranar farko dana ganta a zahiri, dan kuwa tunda nazo gidan bata zoba, dama Dad ya sanarmin batajin daɗin jikintane tana fama da ƙaramin ciki shiyyasa, amma ita bata iya sati ɗayama batazo gidanba. Takun takalminta ya sakani dawowa hayyacina, ƙoƙarin fita take tana sake bina da kallo, sai yamushe fuska take tamkar taga wani kashi ko abin ƙyanƙyami. Da ƙyar na iya fusgo magana a harshena nace, "Sannu da zuwa aunty". Banyi tunanin ta amsa mani ba, ta dai fice da ɗan gudu kamar cikin fushi ko tunanin takalmin ƙafarta zai iya kadata bataiba kuwa.

______________________ JAWAAD ______________________

Ɓangaren Jawaad kuwa yau gidan Alhaji Kokino ya sake kai ziyara, inda ya samu damar ganawa da dattijuwar nan da wancan zuwan ta kawo musu kayan breakfast. Wannan karon ma itace ta kawo masa ruwan sha, dan shi kaɗai ya zo sai gimba. Koda ta ajiye ruwan bayan gaisuwa sai tai yunƙurin juyawa zata fice abinta. "Da alama dai a ranar sha uku ga watan bakwai, dai-dai da washe garin rasa Alhaji wani abu ya faru wanda ganinsa ko jinsa ya jawo Accident ɗin faɗuwa a gareki har kika samu ciwon da har yanzu kike jinsa a jikinki, kuma tabbas wannan abun da kikaji ko kika gani yana da nasaba da Alhajin". Cak ta tsaya, ita bata fitaba bakuma ta dawo da baya ba, ba komai ne ya jawo hakanba sai kalaman Jawaad masu saka rikici ga duk mai alaƙa dasu..... Jawaad dake ƙoƙarin zubama kansa ruwa a kofi ya sake katseta da faɗin, "Abin bana dogon tunani bane mama, abin kawai na sani zan cigaba da riƙe Yazeed har sai nasan dalilin faɗuwarki a wannan ranar, miya tsorataki?, abu na gaba ki taimaki kanki kije asibiti a duba ƙafarki, dan naga har yanzu kina ɗangyasata". Ya kai ƙarshen maganar yana takowa inda take a tsaye. Hakanne ya sakata kallonsa ta kauda kanta da ƙoƙarin haɗiye hawayenta, tace, "Miyasa zaka sakamin yaro cikin al'amarin da baisaniba?". "Mama idan har kina buƙatar na sanar masa komai a yanzu ai bamu makara ba". Idanunta jajur ta ɗago ta kallesa, shima kallon nata yake, amma sai ya janye nasa idanun ganin tana neman rikicewa, yay murmushi yana sake matse kofin hannunsa na glass, rashin ƙwarinsa ne ya saka kofin tarwatsewa sauran ruwan ciki ya jiƙe masa hannu ya zuba a ƙasa, guntayen kofin kuma sukai ɗai-ɗai a ƙasan suma. Dattijuwa ta sauke idonta akan hannun Jawaad har zuwa kofin da yaya kuci-kuci a saman tayis tamkar ba shiba, sake maida kallonta tayi gareshi a wani yanayi mai nuni da tsantsar damuwarta. Jawaad ya zaro handkherchief a aljihunsa ya goge hannunsa tas sannan ya turasu a aljihu duka biyun yana ja da baya fuskarsa na ƙara tsukewa. "A duk lokacin da aka zuba ruwa a glasscup yana da matuƙar ƙayatarwa, har kakanji bakason ɗauke idonka wajen kallonsa koda zaka kwana a haka, amma da tsautsayi zaisa wannan kofin fashewa a hannunka zaka iya gamo da haɗarin yanka maisa aji zafi, shi kuma ruwan dake ciki idan har ya zuba a jikinka ƙoƙarinka kawai ka goge, damshin da ya rage iskace kawai ka iya busar maka dashi, wanda yake a ƙasa kuwa sai kaga dukansa ya zama haɗarine, musamman akan abu mai santsi irin tayis. Na tabbata duk wanda zai shigo falon nan a yanzu zaiyi ƙokarin ganin bai taka wannan ruwan da glasess ɗin nanba, yaron da hankali bai gama bin jikinsa bane kawai zai maidashi abun wasa. Mama bansan yaya zaki rarraba zantukana a jujuwan da suka cancantaba, ni dai kawai abinda raina ya bani komai tsanani zansan gaskiyar zancen...." Ya raɓata ta gefe zai fice, yana saka ƙafarsa ɗaya a waje yajiyo sautin dariyarta. Dakatawa yay tare da juyowa yana kallonta. Tace, "Yarona idan kwalba ta fashe a hannun mutum zafinta kawai zaiji saiko fitar jini da zai gani, amma idan zuciya ta samu suka har abadan wannan tabon baya gogewa komi adadin shekarun da aka ɗauka bayan jin wannan ciwon, ruwan da zai zuba a jiki a goge iska ta busar bashi da banbanci da hawayen dake kwarara daga idaniya zuwa fuska a goge iska ta busar da sauran, inda ake samun banbancin kawai shi wannan ruwane, daya zube labarinsa ya shuɗe, suko waɗannan hawayene koda sun bushe ba'a daina iya ƙididdige su a tsarin da sukazo na farin ciki ko akasinsa har ranarda fitar numfashi zata yanke, ka cancanci a kiraka da suna *Ƙwai cikin ƙaya* sannan kuma lallai ka cancanta a kiraka da suna *Yaro ɓata hankalin dare kayi suna*, duk abinda kake buƙata daga gareni zaka samu, amma ba'a nan gidanba, mu haɗu a gidan daka ɗauki yarona Yazeed.............✍🏻 Typing📲

🧺ƘWAI cikin ƘAYA!!🧺

Bilyn Abdull ce🤙🏻

Masha ALLAH, Alhmdllh, ina fatan kunyi sallah lafiya, to ALLAH ya maimaita mana, duk da dai banga kai da ƙafa na ragunan layyarku ba ballema akai ga an ban naman😥😒. Ga dai ƙwai cikin ƙaya part 1 a kammale waje guda, ammafa kafin na sakesa akwai sharaɗi😂, ƴan Wattpad sunƙi mana subscribing, dan haka ga page ɗaya ku ɗanɗana, daga nan zuwa monday idan naga ruwan subscribers a chennals namu na youtobe tofa nima zan saukesu baki ɗaya💃🏻. Kunce bakwa ganin link ɗin kona saka anan, tom ga hanya mai sauƙi, kuyi Searching tashoshinmu guda biyu masu suna AL-ƘALAMI TV and MANHA HAUSA NOVELS a manhajar youtobe, ku sanƙama mana subscribing tare da sauraren daɗaɗan buks namu Please, ga fili ga mai doki, dan zan koma gefe na tsume naga yaya wasan zai kaya (Subscribers 500🙊) 😂💃🏻💃🏻😻😻😻⛹♀.

___________________________________

SHAFI NA TALATIN

.............Salon rayuwa ya kuma canjawa, ga Bilkisu a matakin da zuciya bata taɓa hasasowa ba, balle sakashi a jerin burin mallaka, mun tsunduma a cikin karatu gadan-gadan babu kama hannun yaro. Sannan kamewar kai babu kula samari ko ƙawayen banza kamar yanda mukaima kammu alƙawari, inhar jerin ɗalibai masu ƙwazone, dolene ka samu sunan group ɗinmu a sahun farko, cikin lokaci ƙanƙani sunanmu yay kuwwar fita sararin subahana a makarantar. Bawai a rashin kunyaba, ko nuna rashin tarbiyya, a'a tamu zarran mu a karatu take da kamun kai. Ɓangaren samari akwai masu bibiyarmu akoda yaushe, sai dai sam basa samun fuska daga garemu, burinmu kawai cika alƙawarin da muka ɗaukama kawunanmu inhar muna cikin masu tsawon rai. A haka kwanaki sukaita ja babu ko gargada a ciki, wataran a mori yini da kwana da farin ciki, wataran a riskeshi da saɓanin haka. Kafin wani dogon nazari watanni biyar suka shuɗe mana, mukazo gida hutun sati buyu. Bazance hutun baimun daɗi ba, sai dai babu wani farin ciki daya bani, dan na iske Mummy tayi tafiya itada Aamilah zuwa wajen aunty Shahudah, hakama Dad baya ƙasar, sai Salman da Qaseem kawai. Tun saukata gidan na fahimci bazai zaunu a gareniba, dan kuwa ni kaɗaice mace a cikinsa, Amina ma bata zuwa kamar yanda Mummy ta bata umarni, wannan damar data samu ne ya sakata nufar ƙauyen babanta taɗan huta itama. Ƙananun ƴan akuyancin da Salman ya fara nuna mini ne ya sakani tattara inawa-inawa tunkan abun yay nisa na fece gidan Inna zainabu kamar yanda na nema izini wajen Dad, nakuma taki sa'a babu musu ya bani dama ba tare daya bincikeni dalilina ba. Ban wani samu gamsashahiyar tarbaba daga wajen Inna, sai dai hakan bai dameniba, dan hakan ya fimin zama cikin ƙattai. Lawisa kam yanda ta shareni nima hakan na shareta, tadai san bata isa sakani wani aikiba a yanzu, dan wannan ba Bilkisun da bace data raina. Nai amfani da damata kuwa, wajen ziyartar gidajen dangin mahaifina harma da sauran na mahaifiyata, duk da kuwa a baya sun nuna basa buƙatata. Wasu a cikinsu sunji kunya sosai ganina a ƙyaƙyƙyawan yanayi, saɓanin abinda sukai mini fata, ni dai ban maida kaiba, koba komai dai na samu ladan zuminci, kuma duk duniya bani da kamarsu. A haka na cinye nawa hutun, Dad ya turo mini kuɗin sayayyar komawata ta hannun Qaseem. Dan haka dole na shirya na koma gida ana saura kwana biyu komawarmu, naji daɗin rashin iske Salman, sai dai shima Yaa Qaseem ɗin yawan kallo da yake bina dashi ya fara takurani, abin mamaki da zanje sayayyama shine ya kaini, sai kuma wani takalata yake da hira, ni abunma sai ya ɗaure kaina matuƙa. Ban dai nuna masa komaiba ko a fuska, na samu muka kammala ya maidoni, tunda na samu na sheƙa ɗakina saina kulle kaina bai sake ganinaba ban sake ganinsa ba. Sai dai bayan isha'i naji ana ƙwanƙwasa min ƙofa, koda na buɗe sai na ganshi, mamaki ya kamani, amma kafin nace wani abu sai cewa yay nazo na dafa masa shayi. Ban masa musuba nabi umarninsa, duk da a zuciyata ƙunƙuni naketayi akan hakan, ga kuku amma ni zaizo ya saka aiki. Abin al'ajab sai ya biyoni kitchen ɗin, yaja kujera ya zauna, ni dai inata neman tsarin ALLAH daga sharrinsa inma dashi yazo, ina gamawa kuma zan wuce ya tsaidani. "Zauna mana, kina ganin gidan shiru babu wani abokin hira shine zaki barni ni kaɗai". Idanu kawai na ɗaga na kallesa, ganin ya kafeni da nasa idanun sai na sauke numfashi kaɗan, nace, "Yah Qaseem kasan ina shirine fa, gashi sammako zanyi idan ALLAH ya kaimu". Kamar bazai tanka minba sai kuma ya sake kallona, baice komaiba ya miƙe yana faɗin, "Muje to kina shirya kayan kina tayani hira". Tamkar zan fasa ihu haka naji, haka ya tasani gaba har ɗakina, ya zauna a kujerar gaban mirror ni kuma ina daga wajen gado saman kafet ɗin wajen ina kimtsa kaya, gaba ɗaya jina nake a takure, gashi ba wani hirar mukeba, ya zubamin idone kawai yana shan shayi, niko ina aiki. Sauri-sauri na kammala nai gefe dasu, cikin kwantar da murya yanda zaiji tausayina nace masa barci nakeji. Murmushi kawai yayi, ya miƙe ba tare da yace min uffanba ya fita. Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi a fili ina faɗin, "Wannan takura har i...n...a..." Na ƙare maganar da ɗai-ɗai saboda tozali danai dashi ya dawo baya, munafukin ashe ba tafiya yayba. Kaina na sunkuyar ƙasa jikina na tsuma saboda tsoro. Sai da ya gama ƙaremin kallo sama da ƙasa sannan ya juya ya fice abunsa. Ai yanzu ko motsi banyiba sai da naja lokaci mai tsaho sannan, cikin sanɗa naje na rufe ƙofar tare da murza key.

Washe gari da safe, koda na idar da sallar asuba ban kwantaba, nai dukkan shirye-shiryen daya dace na fidda kayana waje, ɗaki na dawo nai wanka sannan na shirya tsaf na fito. Nasan dai driver zai kaini, dan haka na nufi wajen motar dana kai kayana. Cikin girmamawa yace, "Ai kayan suna can" yay maganar da nuna motar Qaseem. Da mamaki nace masa, "Can kuma? Mikuma ya maidasu can ɗin Nura?". "Yallaɓai Qaseem ne yace a maida". Kafin na bashi amsa takun takalman Qaseem suka katseni, ba tare daya kalleni ba yace, "Malama ki zagaya mota sauri nake inada wajen zuwa". Tamkar na zauna naita ƙwaɗa ihu haka naji, dole nabi umarninsa naje na shiga inda ya buɗemin da kansa bayan ya shiga. Haka muka tafi tamkar kurame, sai lokaci-lokaci yakan jani da hira, wata na amsa da baki, wata nace, "eh ko A'a". Da haka muka iso. Da kansa ya fito ya taimaka min muka shiga da kayan, ba tare daya zaunaba yace zai wuce. Sake rakosa nayi wajen mota nai masa godiya. Harya tada motar sai yace na bashi wayata. Bashi nayi ina ƙunƙuni a zuciyata, duk da bansan miyayi da itaba naji a jikina number ta ya ɗauka, ya haɗo wayar da kuɗi ya miƙomin. Zan zare wayar ya harareni, dole na haɗa da kudin na amsa nai masa godiya. ★★:★★:★★ Tun daga wannan lokacin abubuwa suka fara sauyawa tsakanina da Yah Qaseem, tun yana kirana lokaci-lokaci harya fara komawa kullum. Banaƙin ɗauka, dan koba komai matsayin yaya yake a gareni, sannan banjin zan iya tozarta zuri'ar Dad, Yah Qaseem kuma namijin da kowace mace zata iya sone, dan akwai ƙyawu, yana aikinsa, tunda nake dashi ban taɓa kamashi da wani abu mara ƙyauba, sai dai idan a ɓoye yake kayansa, wannan kuma ya rage nasa ai, matsalar sa dai rashin ilimin addini, wanda gaba ɗaya ɗiyan dad ya zama babban tawaya wa rayuwarsu, tsagwaron wayewarce kawai da duniya suka sani. Munja kusan shekara ɗaya da rabi a haka, shi baice yan sonaba, sai dai alamomi, dan duk randa ya bushi iska zaizo busting ɗina da kaya niƙi-niƙi, zanma ce yafi kowa ziyarata a gidan, idan kuma naje hutu yata bani kulawa kenan harna taho, ko wani abu Aamilah ko Salman sukaimin sai yayi magana a yanzu. Kulawar da Yah Qaseem ke bani a yanzu na kula tana ɓata ran Mummy, duk da dai bata magana ni nakan hasaso ɓacin rai a fuskarta. Ni kaina take-takensa suna tsoratani, dan ni dai nasan yafi ƙarfina ta kowanne fanni, duk da canjin dana samu a rayuwa bansama raina zan samu koda wanda bai kaisaba matsayin miji, ni dai kullum addu'ata ALLAH ya bani nagari da zai zamarmin mijin marainiya. Muna shekara ta uku a makaranta Yah Qaseem ya fiddo manufarsa fili a kaina a kaina, dan kuwa ya tabbatar min shifa sona yake. Na shiga tsantsar ruɗani da wannan furuci, duk da na daɗe ina hasashen haka, dama a lokacin munje gida weekend ne, ALLAH ma ya soni ana gobe zan komane, aiko washe gari baisan na gudu ba. Koda na sanarma su Ummie sai sukaita zugani akan na karɓa masa, dan Yah Qaseem ya cancanta, idan kuma bana sonshine to, amma sun daɗe su dama suna hasashen akwai wani abu a ransa game dani, sudai suna bani shawara nai amfani da damata gaskiya. Ni dai kasa cewa komai nayi, dan idan nacema banson Yah Qaseem nayi ƙarya, ya fini komai a rayuwa, sannan ya cancanta a soshi, amma idan harna amsa to na ɗeboma kaina gagarumar rigima daga ahalinsa, musamman Mummy da tunkan ya furtama take ƙyamatar abun, inaga yanzun yace yana so. Bai sake bi takaina akan sonjin amsar na aminceba koni ina sonsa, ya dai ƙara ninka kulawarsa kaina fiye da ta baya. Yana cigaba da sakani sakin jiki dashi ba tare dana saniba nima. Shi dai Dad koda ya fahimta baice komaiba, amma Mummy ƙiri-ƙiri ta nuna bazata saɓuba, hakama Aamilah da Salman. Wannan soyayya ta Qaseem ce ta kuma ƙirƙirarmin samubawar tsangwama da tsana a gidan, a wajen Dad da yah Qaseem kawai nake samun sassauci, gashi Dad ba mazauni bane. Cikin wannan yanayin tsangwama muka shiga shekarar ƙarshe a makaranta nida ƴan uwana guda huɗu.