Reader mode
Kwai acikin kaya book 1 Chapter 24
3,847 words
Lallaikam inda rai da rabo inji masu iya magana, to nima dai Bilkisu yanzu na shaida hakan, dan kuwa yau gani cikin jerin waɗanda ake horaswa na hukumar ƴan sandan farin kaya a cikin (Training center) ɗinsu, tare da ƙawayena huɗu a karo na uku. Duk yanda zan fasalta abun ba lallai ku fahimta ba, amma al'amarin ɗanba sauƙine, anji jiki kafin ƙashi da tsoka su saba, yayin da ƙarfin jini da karsashin zuciya ke ƙara yawaita, babu babban maicin ribar abu irin maiyinsa da yaƙini ko fushin son maida murtani. Nayi imani da hakan ya taimakama ƙwazonmu sosai ni da ƴan uwana, dan kuwa matakin farko na nasara damu aka shallakesa, kamar wasa sai gamu a mataki na biyu, inda mataki na uku ya kasance na masu babbar nasara, dan kuwa a cikin waɗanda muka shigo wajen mu sama da dubu biyu bamu wuce mutum dubu ɗaya da ɗari uku muka shallakeba, a kuma cikin dubun muka kasance mafiya ƙwazo mu ɗari uku da ashirin, cikin 300 ɗinan aka kuma rairayemu mu saba'in, mu goma sha uku ne kawai mata a cikin saba'in ɗinan, sauran duk sun kasance mazane, cikin amincin ALLAH kuma ko ina ina tare da ƙawayena. Mu 70 ɗinnan an waremu domin samun horo na musamman fiye da sauran ƴan uwanmu, ƙwazon da muke nunawa da juriya ya samu fita cikin ƴan rukunin farko kenan.
A haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa har suka rikiɗe zuwa watanni, inda cikin amincin UBANGIJI muka cika dikkan shariɗɗan zamowa cikakkun ma'aikata abin alfahari. Tabbas wannan nasara da muka samu munyi matuƙar farin ciki da ita, ranar kuma nasha kuka saboda tunowa da iyayena da siraɗin rayuwa dana tsallake batare da hasashen kaiwa wannan matsayinba na yanzu. Shiyyasa akace babu maraya sai rago, wannan magana tabbas haka take.
★★★★★★
Ranar data kasance ranar yayemu ta zamto rana mai daraja da zuciya bazata iya mantawaba, dukanmu muna cikin Uniform da suka ƙara mana kwarjini da cikar kamala, inda manyan baƙi da manyan wannan hukuma sukai jawabai masu nuna ƙwarin gwiwa a garemu da fatan alkairi, sai ƙyaututtukan karramawa da suka biyo baya na ɗalibai mafiya ƙwazo a cikinmu inda sunana ya fito a bazata. Wannan abu ya sakani ɗunbin mamaki da al'ajabi, dan ban taɓa kawo hakan a rainaba koda a mafarkina, dan ni kaɗaice mace a cikin waɗanda suka samu wannan karramawa. Dad yaji daɗi sosai, hakama Yah Qaseem, su Mummy ma dai dayake duk hardasu akazo sun tayani murna koda bata kai har cikin zukatansuba. Daga ƙarshe kowannenmu ya samu takardar tabbatuwarsa ma'aikaci tare da inda aka turaka, matakin karatu ya matuƙar taimaka mana wajen tsintar kai ba'a matsayi mafi ƙaranci ba, dan kuwa bamu kasance matakin ƙarsheba. Mun rungume juna mu dasu Zuhrah muna kuka, dan kuwa dai an samu matsala wajen rarrabamu bazamu kasance a waje ɗayaba, kowanne da inda aka cillashi, ni da Ummie ne kawai a waje ɗaya. Sosai hakan ya taɓa zukatanmu, har sai da iyayenmu suka koma lallashi da nuna mana ai dama aikin kenan, wannan ba makaranta bace balle muce tilas mu kasance a zaɓinmu.
★★★★★★★
Sati guda cif da gudanar da bikin yayemu muka shiga filin daga, yau sai ga Bilkisu Adam makaho matsayin ƴar sanda ta hukumar DSS, Yah Qaseem shine ya zamemana fitila a komanmu ni da Ummie, duk da kasancewarsa babba a wannan hukuma. Aikin farko da muka fita Ummie tayisa cike da tsoro, ni naita ƙarfafa mata Gwiwa har itama ta samu ƙarfin zuciya, a cikin kwanakin da basu gaza sittin ba, waɗanda a jimlace zasu baka wata biyu mun gama gogewa, muma munaji a ranmu mun isa karanmu yakai tsaiko.............✍🏻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻https://youtu.be/gUGygQ5y5pg
*_MANHA HAUSA NOVELS_*
https://youtu.be/xUINNiDdeH0
*_AL-ƘALAMI TV_*
*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*_____________________________________* *_BOOK ONE_* _Shafi na talatin da biyat😎_ *_____________________________________*
............Yau safiyar Laraba muka tashi da labarin dawowar wasu manyan jami'ai na wannan hukuma tamu kamar yanda manyanmu suka sanar. Na kasance a cikin tawagar masu zuwa tarbarsu da aka ɗiba a cikin mu ƙananun ma'aikata, akwai kuma manyanma. Hakanne ya tabbatar mana lallai waɗanda zamuje tarar sunada muhimmanci a wannan hukuma. Haka kawai na tsinci kaina da faɗuwar gaba, zuciyata sai wani irin zallo take kamar zata faɗo ƙasa. Ƙirjina na dafe ina lumshe idanu, dama tun jiya nakejin tamkar wani gagarumin abu na kusanto rayuwata, sai dai bansan minene ɗinba. Mun iso airport ɗin akan lokaci, dan jirginma bai kai ga saukaba sai nan da minti arba'in kamar yanda aka sanar damu. A yanda mutane suke kallonmu musamman ma mu matan da muka kasance mu biyu kacal yasa duk na takura, sanye muke da Uniform wanda ni kaina nasan sunma surata matuƙar ƙyau, tabbas bani da ƙyawu mai tsanani amma ALLAH ya azurtani da ƙyaƙyƙyawar surar dake da wahalar samu ko a cikin matanma, wadda itace ke fisgar maza da yawa a gareni, akwai baby hijjab dana saka kafin na ɗora hular Uniform ɗin a saman kaina, hakan ne zai baka amsar kasancewata musulma kai tsaye. Addu'a na rinƙayi a zuciyata, saima na saka eyeglasess a idona saboda kallon ya gundunreni. Adadin mintuna na cika jirgin da muke tabbacin jira ya iso, saida ya gama shawagi a sama kafin ya sauka a inda ya dace, wannan shine karon farko da nazo airport a rayuwata, hakan ya sakani tsarkake sunan UBANGIJI daya sanya fasaha ga zukatan waɗanda suka ƙera jirgi, sannan ya bashi ikon tashi sama duk da girman da yake dashi. Bugun zuciyata ya sake sauya salon bugawa da sauri-sauri, hakan ya sakani rumtse idanu dukkan jikina na wata irin tsuma, haka kawai sai nakejin kamar na kama kuka. Taɓanin da akaine ya sakani buɗe ido da sauri, ɗaya daga cikin ma'aikacinmu ne da yake nema takurama rayuwata, na kallesa ina ɗauke kaina dan haushi yake bani, shi a dole wai sona yake, tun a wajen training ya maƙalemin, sai kuma akai rashin sa'a muka tsinci kanmu a waje guda. Ganin ya gyara tsayuwa zai fara magana nai gaba abuna. Dai-dai fasinjojin jirgin sun fara fitowa. Duk wanda ya fito a jirgin idonmu a kansane, sai dai ganin babu wanda ya motsa daga jami'anmu ya tabbatarmin namu tawagar basu fitoba har lokacin. Sai da kowa ya gama fitowa har babu alamar sauran mutane kafin wata mata da yara biyu ta fito, sai wata kuma a bayanta ita riƙe da hannun yaro namiji, sai wata na biye musu baya itama. Suma sai da suka sauka duka sannan sannan fitowar wani sadauki da tai daidai da tsananta bugun ƙirjina ya fito. Zaratan mazaje uku da doguwa budurwa na biye dashi a baya. Jinai ƙafafuna na neman gaza ɗaukata, hakan yasani saurin jingina da ɗaya a cikin motocinmu gudun karna faɗi.
Jawaad dake fitowa ya sauke idanunsa akan sir Ahmad barewa, kafin yaci gaba da bin ma'aikatan tadabbaci ke nuna sunzo tarbarsu ne. Kansa tsaye inda su sir Ahmad da wasu manya suke suka nufa, inda shima Sir Ahmad ɗin ya nufesu fuskarsa cike da fara'a da farin cikin ganinsu. Gaba ɗaya sauran ma'aikatan sukaja layi alamar girmamawa, miƙewa nai ina sauke numfashi tamkar wadda tai gudun fanfalaƙe. Sai da ya gama gaisawa da manyansa kafin su nufomu su dukasu. A tare muka buga ƙafafu tare da yin salute nasu cikin nuna tsantsar girmamawa.
Jawaad dake tsaye yana ƙare musu kallo idonsa ya sauka kan matashiyar budurwa mai hijjab. Ganin ya tsura mata idanu Jabeer da suke bayansa yay mata umarni data cire glasses ɗin idonta a ɗan kausashe. Kawai jinai idanuna sun cika da ƙwallan da bansan dalilinsu ba, na zare eyeglasess ɗin idona kamar yanda aka umarceni tsigar jikina na wani irin tashi tamkar nai gamo da halittar ban tsoro. Babu zato idanuna suka shige cikin nashi idanun masu wani sinadarin da baki bazai iya faɗaɗa bayani akaiba. Kasa jurewa nai na janye nawa ina rissinar da kaina tamkar zuciyata zata faɗo ƙasa. Shima cikin basarwa ya janye nasa idanun cikin wani salo na halin ko in kula. Sai da ya gama ƙare mana kallo mu duka kafin yay guntun murmushin daya saka kumatunsa loɓawa. Saitin inda nake yay mana nuni da hannu alamar mu bashi hanya, hakan ya sakamu darewa muka rabu biyu ya gittamu ya wuce, mayen ƙamshin turarensa na rige-rigen shiga ƙofofin hancinanmu. Da sauri wasu a cikinmu suka nufi motocin suka bubbuɗe musu har manyan mu da mukazo tare wajen, ni dai bamma iya koda motsiba daga inda nake, saboda bani da wani ƙarfi sam balle samun kuzarin yin abinda ya dace. Sai dai idona akan motar daya shiga shi kaɗai baya aka maida aka rufe masa, haka kawai naji tamkar ana kallona, kallo kuma irin na ƙurilla, sai dai iya dube-dubena banga alamun kowa da idonsa ke kainaba, saboda mutane sunata hada-hadarsu ne. Hannu na ɗora a hankali bisa ƙirjina dai-dai saitin zuciyata ina lumshe idanu, wasu ƙananun hawaye suka silalomin a kan kumatu, saurin jan hulata nai sosai yanda zata hana kowa kallon halin da nake ciki kafin nasa handkherchief na share cikin dabara ina nufar mota nima.
Jawaad da tunda ya shiga mota idonsa ke akanta yana ƙare mata kallon da shima baisan dalilinsa ba ya lumshe idanu yana huro iska ta ƙofofin hancin, kuma buɗewa yay sai yaga wayam babu ita a wajen, cikin halin ko in kula yaɗan taɓe baki yana ɗauke idanunsa daga kallon wajen ma baki ɗaya ya maida ga wayarsa.
Tanda muka fara tafiya nake jerama kaina tambayiyin da bansan amsarsu ba. "Miyasa nakejin tsoro? Miyasa yay min kwarjini fiye da kowa? Miya sakani kuka? Minene ma'anar halin dana shiga bayan banida wata alaƙa da wani abu daya taɓa shafar irin wannan yanayin dana tsinci kaina a ciki balle nace na tunashine?". Waɗanan tambayoyi su naita jerama kaina har muka iso, tarbar da muka iske an shirya musu ananma ce ta sakani samun damar zare jiki na koma can gefe na zauna ina maida numfashi da addu'ar samun daidaituwar wannan baƙon yanayi nawa da baida alaƙa da komai. Dafanin da akayine ya sakani juyowa, Ummie ce, hakan yasa tana zama sai kawai na fashe mata da kuka. Ɗunbin mamaki ya bayyana a fuskar Ummie, tai kasaƙe tana kallona tamkar wata sokuwa, "Bily lafiyarki kuwa?". Ban bata amsaba, saima ƙarfin kukana dana ƙara, tai shiru kawai ta sakamin ido, saida nayi mai isata nai shiru dan kaina sannan ta sake jefamin tambaya. "Bilkisu mike faruwa ne wai? Ko an miki wani abune da kuka tafi?". Kaina na girgiza mata alamar "A'a". Tace, "To minene ya faru? Ko baki da lafiya ne?". "Lafiyata ƙƙalau kawai na tuna su babane" na samu kaina da mata ƙarya batare danasan dalilin hakanba, dan nasan bama ɓoyema juna abu sam. Numfashi ta sauke tana dafani, cikin tausasa murya ta shiga lallashina damin nasihar addu'a su baba ke buƙata bawai kukana ba. Kaina na ɗaga mata kafin nace, "Nagode Ummie, insha ALLAH bazan sake yiba". Tai murmushi tana canja akalar firar tamu zuwa wata, "Kutt Bily basawannan namu da kuka tarofa sunji gishiri da magi, musamman mai green ɗin Suit ɗinnan". Gabana ya sake faɗuwa jin ta ambacesa, amma saina danne cikin ƙaƙaro murmushi nace, "Kingani ban wani tsaya ƙare musu kalloba, yanzu haka babu kamannin wanda zan iya kawowa a cikinsu". Tace, "Tab, amma lallai kinyi gwari dan wlhy anci kasuwar sama babuke Babie, ai har sunan mai green suit ɗinma na riƙe". Kallonta nayi da mamaki, tare da jin zuciyata tai zallo, kamar na tambayeta yaya sunan sai kuma na taɓe baki ina miƙewa, "Kinga dan ALLAH bar wannan shirmen tashi muje, yaushe kika fara lalacewa ne haka Ummie?". Dariya ta tuntsire da ita tana dukan kafaɗata, tace, "K nakai aurefa, sannan dukkan burikanmu sun cika, miya rage mana kuma? Musamu mazajen aure kawai, kodan ke kin samu Yah Qaseem a hannune". Kallonta nayi a wani irin yanayi jin ta ambaci yah Qaseem, sai ban iya furta komaiba nai gaba abina ina murmushin ƙarfin hali. Itama bata sake maganaba ta biyoni da hanzari muka dai-daita tafiyarmu.
Da ɗan aiken Yah Qaseem mukai karo akan naje yanason ganina. Haka kawai sai naji kiran yaban haushi, amma bani da damar ƙin zuwa ɗin. Na kalli Ummie ina faɗin, "Dan ALLAH ki rakani tawan". Baya tai tana zaro idanu, "Wa? Rufamin asiri hajiyata, wannan fagen na masoyane ai, aidai ƙone ƙaɗan babie kar ai ƙurmus dan ALLAH". Harara na zuba mata kafin na wuce ina zare hular kaina na riƙe a hannu. Koda na isa Office ɗin nasa kaina tsaye na shiga, dan ya bada sharaɗin shigata babu shamaki. Kallo ɗaya naima fuskarsa na fahimci ransa a ɓace yake, na zauna ina gaidashi cikin girmamawa kamar yanda na saba. Bai amsaba sai numfashi daya sauke, ya taso daga kujerarsa ya dawo inda nake shima ya zauna a ɗayar kujerar dake kallon wadda nake kai. Idanu ya tsuramin kusan minti ɗaya, niko na gaza kallonsa saima takura da nayi, cikin son katseshi na shiga gaishesa. Nanma numfashin ya kuma saukewa yana janye idanunsa a kaina. Ba tare dana kallesanba nace, "Yah Qaseem lafiya dai ko?". Siririn tsaki yaja yana haɗawa da ƙaramar ƙwafa, "inafa lafiya wannan banzan ya dawo". Da mamaki nace, "Banza kuma? Wanene banza yah Qaseem?". Tsakin ya kuma ja yana maido kallonsa kaina, "Bazaki taɓa ganewaba, dan haka share, ina kikaje ɗazun na aika kiranki akace kun fita?". Zamana na gyara cikin rashin damuwa nace, "Ba inda naje, kawai tarbar waɗanan jami'an namu da suka dawone........." "Kina nufin dama dake akaje?" Yay maganar cikin tare numfashina tamkar zai haɗiyi harshensa. Da mamakinsa na ɗaga kaina kawai. Sosai ɓacin rai ya kuma bayyana a kan fuskarsa, ya furzar da ɗacin da nakeda tabbacin yanaji tare da miƙewa. Nidai uffan bance dashiba saima kallo dana bisa dashi kawai. Bansan miya tunaba ya juyi yana faɗin in tashi muje muci abinci. Tashin kuwa nayi, ya fita ina biye dashi, koda muka fito a Office ɗin sai ya tsaya muna tafiya a tare. Bugawar da zuciyata tayine ya sakani komawa tafiya da sassarfa, ɗago idon da zanyi idona suka sauka akan mutumin ɗazun da mukaje tarba. Da ƙyar na iya haɗiye yawun daya tsinkemin a cikin baki saboda kallon ido cikin ido da mukaima juna, amma sai ya janye nashi tamkar bani yake kalloba ya shige motar da aka buɗe masa wadda alamomi suke nuna zai tafi gidane maybe. Nannauyan numfashi ya kufcemin wanda yay dai-dai da fitar sautin jan tsakin da Yah Qaseem yayi...........✍🏻
Karku manta da sunayen chennals ɗin namu.
https://youtu.be/gUGygQ5y5pg
MANHA HAUSA NOVELS
AND
https://youtu.be/xUINNiDdeH0
AL-ƘALAMI TV.
Tashoshin dake manhajar youtobe, zasuke kawo muku dadaɗan buks namu insha ALLAH, Please a garzaya dan ALLAH.
Subscribe Like Shere Comments Watch
And danna ƙararrawar sanarwa domin samun shirye-shiryenmu da zaran mun ɗora😍😍😘.
A taimaka kada yawan masoyan da nake gani anan ya zama na bogi🤗, mutane 5k + amma ko mutun 1k su gaza nuna mana ƙauna😪😪, Please and Please my guys maida murtanin soyayya ga masoyi abin alfaharin masoyane.😘😘😘🤓😻😻
Ga shafi na 35 nan, saura biyar a jakata bazan zuge zip ba sai naga ruwan subscribers😎🏃🏃💃🏻
*_ZAFAFA SABON KAFCE SUN DAWO GAREKU_*
_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_
_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_
_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_
_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_
_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_
_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_
_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_
_GUDA DAYA DARI BIYU_
_GUDA BIYU DARI UKU_
_GUDA UKU DARI HUDU_
_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_
_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_
*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*
2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_
saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863*
*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇
*09032345899*
_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻https://youtu.be/T8bCANmJA5E
*_MANHA HAUSA NOVELS_*
https://youtu.be/xUINNiDdeH0
*_AL-ƘALAMI TV_*
*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*__________________________________* *_BOOK ONE_* _Shafi na talatin da shida_ *__________________________________*
.............Har muka isa wajen da kullum Yah Qaseem ke kaimu cin abinci anan kusa damu fuskarsa babu walwa, bama muba kusan duk anan manyan jami'an kecin abincin, dan wajene haɗaɗɗe da yasha gyara na musamman, sanan ake abinci mai tsafta da daɗi, sai dai kamarmu ƙananu da ƙarfinmu bai kaiba akwai wani gidan abincin daga ɗayan gefen mukanfi yawan zuwa acan muci. To nidai bamma taɓa zuwa wancan ɗinba, dan kullum nan Yah Qaseem ke kawoni, idan kuma aiki yay masa yawa yakan saka akai masa office muci acan kamar yanda wasu daga cikin manyan keyi. Kallon bawan ALLAHn can da yaymin lokacin dazai shiga mota ya mugun tsayan a ƙahon zuciya, duk yanda naso turesa hakan ya gagara, sai sauke ajiyar zuciya nake ina tsakurar abincin badan yaymin daɗiba. Shi kansa Yah Qaseem na lura bawai cin abinci yakeba sosai yau, dan ransa a ɓace yake, na kuma rasa dalilin hakan sam. Haka dai muka tsakura sama-sama muka bar wajen, kafin mu wuce na roƙesa muyima Ummie takeaway. Atm ɗin nasa ya miƙamin kawai ya fice, na bisa da kallo ni dai kafin na amsar mata abinda nasan tanaso na fito, sai dai zuciyata na mamakin miya fusata yaya Qaseem haka wai ne?. Ban iskeshiba hakan yasa na tafi ni kaɗai, dan da alama ya shige abinsa.
Yau bamu bar Office ba sai kusan takwas na dare, tare da Yah Qaseem muka tafi gida, sai lokacin ne na bashi ATM card ɗinsa, inason tambayarsa mike damunsa? Amma wani gefen zuciyata na karantamin na sharesa kawai. Sharesan kuwa nayi nama maida hankali wajen cheating da Rebecca da taimin magana. Har muka isa gida ni da shi bakin juna bai saɓaba, yanata driving ɗinsa, duk da na lura akwai tuƙin ganganci a ciki, wanda na jima da fuskantarsa ya haddace gudu a titi tunba yanzuba. Amina ta taɓa bani labarin yanada driver da aka bashi na office da, sai dai rashin haƙurinsa yasa ya sallami direban, ya gwammaci ya tuƙa kansa da kansa.
★★★★★
A gidanma haka yayta tsumewa, nidai koda na gaida su Mummy dake falo ɗakina na shige, dan yanzu ganin batason sakarmin fuska sai na sake janye mata, aikin dake a gabanama ya isheni gayya basai an haɗamin da damuwa mara dalili ba. Sai da nai wanka naji daɗin jikina sannan na fito falon domin neman abinci, ganin abinda aka dafa a gidan, ni kuma ba sonshi nakeba sai kawai na haɗa tea. Ina daga dani ina shan tea ɗin nake jiyo hirar Mummy da yaranta, harda Yah Qaseem daya zama ginshiƙin hirar, shima da alama yana yin wanka fitowar yayi, jinai yana sanar mata wai Jawaad ya dawo. Da yake ban fahimci kan maganar tasuba sai bansan akan wa yake maganaba, ni dai nayima na tashi na shige ɗaki abuna dan na kwanta na hutama rayuwata. Dan tunda na fara aikinnan Yah Qaseem ke tafiya dani da dawo dani a motarsa Mummy ke haushi dani, inaji ranar tana masa faɗa akan hakan, harma da gargaɗi akan ya fita harkata, inba hakaba kuma yay kuka da kansa. Bandaiji ya tanka mataba, bai kuma fasa ɗaukata a motarba. Niko ina ruwana, tunda bani tama gargaɗinba banbi takai ba na cigaba da binsa kamar yanda Dad ya faɗamasa ya ringa tafiya dani da ɗakkoni tunda ALLAH yasa wajen aikin namu ya kasance ɗayane.
_________________________ JAWAAD _________________________
Tarba maiban mamaki Jay ya samu ga ahalinsa, dan kuwa hardasu Umma duk sun taru a family house nasu. Danne mamakinsa yay shima ya nuna girmamawa ga wannan tarba tasu, bayan gama amsa sannu da zuwa suka bashi damar shiga sashensa domin watsa ruwa. Kaya yake cirewa yana jan ƙaramin tsaki shi kaɗai.
"bansan miya kawo dalilin yawan tsakinba ni kaina, sai dai mucigaba da bibiyar jay ko zamu sami amsa"😉😹⛹♀.
Yanda aka gyara sashen da ƙamshin da yakeyi ya ƙayatar dashi, sai dai yanaji a ransa aikin nan sai dai idan batool ɗin Umma ko Nabeelah wani yayisa. A wajen wankanma ya samu nishaɗi saboda yana son tsafta a rayuwarsa, ya dai gama ƙaƙale-ƙaƙalensa ya fito ɗaure da tawul yana tsane jikinsa da ƙarami. Sosai jarumin na Shahudah ya kuma canjawa, dan dai-dai da gaɓoɓin jikinsa sun sake murɗewa, ga wata gogewa da fatarsa ta sakeyi, yanda ruwa ke gudu a jikinta zai tabbatarma da mai kallonsa hakan. Komai yana yinsane a yanayin gajiya, inda son samune kwanciya zaiyi ya hutama ransa basai ya sake fita a waccan hayaniyarba. Amma yaya ya iya, dolene ya koma kamar yanda suka buƙata tunda sunce danshi suka taru. Sama-sama yay ƴan shafe-shafensa ya saka wando da riga ruwan siminti marasa nauyi, kayan sun masa ƙyau tare da fidda ainahin ƙirar da UBANGIJI yay masa, ya fesa turare kaɗan sannan ya fito harabar gidan daga can baya inda dama anyi wajenne domin hutawa, an gyarashi sosai da korayen ciyayi da filawoyi masu ƙamshi. Sam Jawaad baya zuwa wajen, saboda ƴammatan gidan sun maidashi lambun shaƙatawarsu ko ajiye samarinsu suyi hira, shi zaima iya rantsewa tun bayan daya mallaki hankalinsa baizo wajen sau ukuba, mantawama yake dashi gaba ɗaya, zuwa ukunma da yake kyautata zaton yayi shima duk mitin ne da Uncle's nashi suka shirya ya halarci wajen a wancan lokutan.. Sosai kuwa walimar cin abinci aka shirya, sai dai ya fahimci tamkar da biyu ne, danshi jami'in tsarone mai matuƙar basira da kaifin tunani, hakanne ya taimaka masa wajen gayyato ɗunbin nasarori a cikin rayuwar aikinsa. Yanda ƴammatan Family ɗin nasu kowacce taci ado na ƙure wankane ya sashi fahimtar komai a buɗe. Yay ƙwafa a zuciyarsa kawai yana sake shan toka, baisan miyasa akeson takurama rayuwarsa da awaɗanan yaranba, dan haka sukai maƙurar takura masa ta waya yanacan, kullum babu fashi sai yaga text messeges nasu ɗaya bayan ɗaya, harda masu masa a shafukansa na yanar gizo. Bai taɓa kula koda ɗayarsu ba, danshi a ganinsa hakan rainine. Ƙin cin komai yayi a wajen sai kunun aya kawai, wanda Batool ta tabbatar masa itace ta haɗa masa shi, dan dogon tabirne aka ajiye sannan aka zagayesa da kujerun da adadainsu yakai Hamsin koma fin hakan, manya maza da mata na family ɗin kowa ya samu muhallin zama, su kuma yaran an shimfiɗa musu leda mai ƙyau a ƙasa anan suke nasu shagalin bisa kulawar ma'aikatan gidan. Sai da ya gaji da harar da Umma ke masa akan cin abinci sannan ya ɗau cokali badan yaso ba ya fara cin abinda yasa aka zuba masa cikin nutsuwarsa. Sai dai yanda yay kicin-kicin da fuska ya saka dukkan ƴammatan dake fama da rawar kai suka nutsu, dan dama sunsan shi baya son wargi, bakuma shiga sabgarsu yakeba tun fil azal. Sai dai sai faman satar kallonsa suke ta wutsiyoyin idanu, shiko baima san sunaiba, abincinsa yakeci yana ɗan jefa magana cikin hirar mazan gidan sa'anninsa. Dukda shine ƙarshen fara cin abincin shine kuma farkon fara ajiye cokali, babu wanda bai bisa da kallon mamakiba amma sai ya fuske cike da basarwa kamar baisan miya aikataba, sam saima yaƙi kallon sashen Ummah balle ta sake sakashi tilas akan yacin.