Reader mode
Kwai acikin kaya book 1 Chapter 7
4,500 words
Ya isa ƙofar kurkukun (Jail) da abokansa uku kuma aminansa suka tsinci kansu a ciki dalilin ƙaddara, dan kuwa shekarunsu na biyu kenan a wajen bisa sharri da akai musu dan a durƙusar da Jawaad ɗin, yayi iya bakin ƙokarinsa a lokacin ganin sun kuɓuta amma sai hakan ya gagara, dankuwa ƙulline mai cike da ruɗani a ka ƙulla dan kawai a dakusheshi tunda ansan abokansa suna cikin manyan abinda ke ƙara masa ƙwazo da ƙarfin gwiwa, duk yanda yaso gano wanda ya aikata masa hakan kuma bai samu nasaraba, shiyyasa ya tattara komai ya maida hannun ALLAH, sai gashi a yanzu cikin sauƙi ALLAH ya kuɓtar dasu. Shigarsa wajen ta saka ma'aikatan gidan yarin bashi girma na musamman, dan sunsan wanene shi da matsayinsa, tunda dama jail ɗin bana kowa da kowa bane, jami'an tsaro masu laifi kawai ake sakawa a ciki. Bayan shigarsa Office ɗin shugaban wajen na wasu mintuna aka kammala komai, yana nan zaune aka fito dasu. Idanu suka tsurama juna da ga shi harsu, tuni idonsa ya kaɗa yay jazur tamkar an hura barkono, jijiyoyin kansa sunyi wani irin fitowa ruɗu-ruɗu, ya miƙe ahankali yana tunkararsu tamkar yanda shima suke nufoshi cikin wani irin yanayi na kewa da farinciki, dan shekaru biyun da suka ɗauka a rufe sam an hana Jay ganinsu. Rungume juna sukai su huɗu, dukda yanda jikinsu yake baiji ƙyamarsuba, kowanne hawaye masu raɗaɗi suna kwarara a idanunsa. Su dai ma'aikatan wajen kallonsu kawai sukeyi. Kusan mintuna uku suna a haka, kafin su ɗago kowanne yana ƙokarin sharema ɗan uwansa hawayensa, sai kuma suka sake rungume juna suna dariya saikace wasu zararru. Nanma kusan sakwan arba'in suka ɗauka kafin suyi haramar fitowa ba tare da ko bakin ɗayansu ya saɓa ba wajen furtama juna magana. Gimba dake jikin mota tsaye ya hangosu suna fitowa daga cikin Jail ɗin a yanayin da yasansu a baya, jarumai kuma aminai, sannan ƴan uwan juna masu ɗaukar kansu JINI ƊAYA. Cike da wani irin ɗoki yake washe musu baki har kunne, lallai yau farin cikin boss ɗinsa sun dawo, yanzu sauyi zai sake zuwa a hukumarsu, hannunsa ya dunƙule waje ɗaya yana cigaba da washe bakinsa, yama kasa magana saboda tsabar farinciki. Suka dafashi a kusan tare suna dariya suma. Da ƙyar ya iya furta, "ALLAH mun gode maka, yau ga basawan boss sun dawo gareshi, tarkon da makiya suka kafa ya buɗe". Jawaad da fuskarsa babu walwala ya girgiza kai kawai ba tare da yace komaiba ya buɗe mota yana musu nuni dasu shiga. Basu ɓata lokaciba suka bar wajen zuwa gidan Jay ɗin dake Empty babu kowa ciki, gidan yayi ƙyau sosai, gashi anguwar da yake babu yawan hayaniya. Suna shiga gidan dukkan farin cikinsu da suka danne da kewar juna sai ya bayyana, dan sake rungume juna sukai a tare kowa na faɗo yanda yay kewar ɗan uwansa. Tsawon lokaci suka ɗauka a haka har Gimba ya dawo da ledojin abinci ba tare da sunsan zaiyi wannan ɗawainiyarba. Godiya sukai masa duk da kuwa yana ƙasansu, ya nuna musu hakan ba komai bane tare dajin daɗinsa na murna da sukai, ya jajanta musu da addu'ar ALLAH ya kiyaye gaba. Wanka suka shiga su duka a mabanbanta banɗakin dake cikin gidan, sun ɗauki tsawon lokaci, dan Jawaad ma harya fice zuwa wani kiran gaggawa daya samu daga office ya barsu akan kafin ya dawo su tabbatar sunci sunsha sun huta.......
______________________ BILKEESU ______________________
.........Har dare babu labarin bilkisu a cikin anguwar, ga kuma ƴan sanda ta ko'ina an bazasu nemanta, sai kuma yaran Jazuuga dasuma ke aikinsu domin taya ƴan sandan.
Ina cikin mankarar har dare, tun ina kuka da hawaye da murya harna koma na zuciya kawai nake iyawa, hankalina bai gama tashiba sai da na farajin motsin mutane masu shigowa sallar magriba, kuma nutsuwa nayi a wajen duk da ƙarfina ya ƙare, hannuna dafe da bakina gudun kar wani mai ƙarfin ji ya iya jiyo fitar numfashina. ALLAH ya aramin wannan lokacin har akai sallar magriba aka kammala. Sosai ƙarfina ya gama ƙarewa, na gaji da tsaiwar, burina kawai na zauna nahutama raina, ƙafafuna sunyi nauyi tamkar ba'a jikina sukeba, gashi wasu suna a massallacin basu gama ficewa ba, sun zauna har sai anyi sallar isha'i. Haka na cigaba da dauriya a wannan yanayi mai wahalar musaltawa har lokacin sallar isha'i yayi ya wuce, mutane sun fara barin massallacin, inda akabar tsirarun da suka koma fita ɗai-ɗai. Wani da ya fita na ƙarshe shida abokinsa naji suna faɗin ƙarfe goma da rabi na dare, bana a hayyacina zuwa lokacin sosai, amma bayan fitarsu da wasu mintuna saina leƙo kaina cikin massalacin, babu kowa sai mutum ɗaya dake barci, da gyar na tattaro ɗan sauran ƙarfina na janye mankarar na fito, tafiya nake tamkar bugaggiyar da tayi mankas da kayan maye, ni kaina bansan a ina nake jefa ƙafaba, tafiya kawai nake tamkar bahagon raƙumi. Ƙwaƙwalwar kaina sam bata aiki da zuciyata, ni kaina na fara manta wacece ni?. Ƴan sanda biyu dana hango gabana suna tunkaroni yasani firgicewa, nai saurin komawa baya na maƙale jikin bangon wani gida, ta gabana sukazo zasu wuce suna magana wadda na fahimci akainace. Ɗaya a cikinsu ke faɗin, "Oga kana ganin Alhajin nan zai bamu maƙudan kuɗinnan kuwa daya faɗa inhar aikinnan ya kammala yanda akeso?". "Hhhh bayarwa kuwa zaiyi ɗan sambo, bakaga yanda yake a firgiceba, bashi da burin daya wuce akama yarinyar, sannan ɗansa ya kuɓta, shiyyasa nima nace muyi ƙaimi, dan inada tabbacin tana cikin anguwarnan bata fitaba, sai dai idan wani munafikinne ya bata mafaka a gidansa". "Shegun ba, ai zamu kamatane, idan kuma har kuɗinan suka tabbata lallai lokacin ƙara aurena yayi kenan, dan wlhy zama da kubra kawai nafi ƙarfinsa". "Hhhhhhh!! Wato ɗan sambo shiyyasa nake sonka wlhy, kai abokin neman arziƙine, idan kana abu sainaji daɗi saboda lallai kana kan tsarina, saikace uwa ɗayace ta haifemu". Dariya suka kwashe da ita tamkar wasu mahaukata su duka biyun, da wannan mahaukaciyar dariyar suka wuceni batare da ɗayansu ya hankalta dani ba. Numfashi na sauke cikin gajiyawa, sai da na tabbatar sun ɓacema ganina sannan nacigaba da tafiya ina zirar da hawaye, wace irin ƙasa muke da ita hakane? Masu bada tsaro da kariya sune suka koma masu ɓata tsaro da zalunci?. Ta yaya har muke tunanin samun shugabanni adalai bayan muma talakawan azzaluman junane?. Nacigaba da tafiya ba tare da namasan ina nakeba, abinda na sani kawai shine nayi nesa da anguwarmu kam tabbas, sannan ina buƙatar zama na huta, sai dai tsoro da fargabar kar azo a kamani sun hanani damar samun wajen yada zango.
Nayi tafiya mai nisan gaske, wadda sam banida nutsuwar ƙididdigeta koda da ƙiyasine, tun ina gamuwa da mutane da kallon motoci a titi har garin ya fara ɗaukar shiru, bakaji koda ƙarar mashin, ƙafa tafara ɗaukewa, hakama motoci, lokacin da garin ya gama ɗaukar shiru babu abinda kakeji sai haushin karnuka. Da ƙyar na iya kawo kaina wani wajen da nakeji sautin kiɗa na tashi, duk yanda naso samun dauriyar matsawa daga nan na kasa, cikin rashin kuzari da ƙarewar ƙarfi na zube jikin wata bishiyar mangwaro dake a gaban gidan, mashina ne birjik a wajen duk an faka, sai jefi-jefi na mutane dake fitowa daga wajen mace da namiji ko mata zalla. Tun ina kallonsu har na gazama hakan, idanuna da sukai nauyi jingim saboda kukan da nasha na lumshe a hankali, badai barci nakeba, bakuma ina tare da duniyar mutane bane sam. Tsawon lokaci ina a wajennan ba tare dana fargaba, sama-sama naji ana tadani, na buɗe idanu da ƙyar ina saukesu akan ƴanmata biyu da bazasu gaza sa'annina ba, sai namiji dake gefe yana faɗin, "Ƙila tasha abinda kanta ya gaza ɗaukane ko?". Ɗaya a cikin ƴanmatan da ke ƙokarin taimakamin na tashi tace, "Anya ma wannan kuwa bamma santa ananba sam, dan inaga baƙuwace". Kaɗan ɗayar ta ɗan haskani da fitilar wayarta rakani kashi, ta kautar da hasken daga fuskata tana cewa, "A gaskiya baƙuwace, dan nima bamma taɓa ganintaba a gidan wasannan". "Da wannan surutun da kuka tsaya da kamata kukai mukaje da ita gida, dan tabbas tana bukatar taimako" namijinne yay magana cikin nuna kulawa. Basuce komaiba sai taimakamin da sukayi na miƙe tsaye sosai, ni dai ban iya cemusu uffanba, suka kamani a kafaɗinsu mukabi wani lingu. Banwani damu da inda suka kawoninba, duk dama gidan tsitt yake alamar duk anyi barci, namijinne yasa key ya buɗe ɗakin suka shiga dani ciki. Sun kwantar dani a katifar ɗakin wadda halin danake ciki baisa na fahimci komai akantaba. "Ƴar daɓas kunna risho a dafa mata ruwa tasamu tai wanka, dan a halin da take ciki na fahimci bazata iya jin daɗin barciba". Da to wadda aka kira ƴar-daɓas ta amsa, cikin mintuna kalilan aka haɗamin ruwan wanka mai matsakaicin dumi, yanzuma da taimakonsu na shiga banɗakin dake a cikin ɗakin. Ban cutar da kainaba na daure nayi wankan, naji daɗin hakan sosai, bayan nagama na ɗauki doguwar rigar da aka ajiyemin na saka sanann nayo alwala na fito, dan yin wankan yasa naɗan fara dawowa a hayyacina. Zaune na iskesu sunacin nama, na ɗan kallesu na duƙar dakai ina faɗin, "Dan ALLAH ku taimakeni da abin salla da hijjab". Ganinai sun kalli juna a wani irin yanayi na shakku, ni saima na fara tunanin koba musulmai bane....... Ɗayar ta katsemin tunani da faɗin, "ƴar uwa samun abin salla a ɗakinnan lallai babban abune, ke ama gidannan gaba ɗaya zance, amma dai ga ɗankwali idan zaki iya maneji dashi, hijjab ma inaga za'a iya samun wanda nazo dashi a farkon zuwa gidanan, tunda kuma na ajiyeshi ban sake waiwayeba". Ban fahimci zancen nasuba, bankuma tambaya ba, inadai tsaye aka bani hijjab da ɗankwalin, shinfiɗawa nai na tada salla, sai da nayi sallar la'asar da banyiba da magrib sannan nai isha'i, harma da shafa'i da wutiri, hannuna na ɗaga sama ina addu'a hawaye masu zafi na kwarara saman kumatuna, nakai tsawon lokaci ina kaima ALLAH kukana, kafin na miƙe. "Wai, wannan salla taki akwai tsawo, zokici abinci muɗan kwanta, dan gari gab yake da wayewa". Yunwa nakeji, hakan yasa banyi musuba nai zaman cin naman da sukaci suka ragemin, sai fura mai sanyi wadda naji daɗinta sosai. Ina kammalawa suka nunamin wajen kwanciya.
Sai a yanzune dana samu nutsuwa komai ke iya dawomin dalla-dalla, wasu hawaye ke sauka saman fuskata a gurguje, koyaya Firdausi take? Inna da baba da sauran ahalin gidanmu, na ɗago hannuna ina kallo zuciyata na wata irin suka, ni Bilkisu yau nice matsayin wadda tai kisan kai, wai ni na kashe mutum?.... Kuka mai ƙarfi ya ƙwacemin, nanfa na shiga rairashi babu mai lallashi, dan masu masaukin nawa bansan ya akai daga kwanciyarsu barcinsu yay nauyi irin hakaba, na daɗe ina kuka har aka kira sallar asubahi a kan kunnena. Tashi nai cikin layi da nauyin jiki nayo alwala, nazo ina ƙokarin tashinsu amma sam babu wadda tai motsin kirki balle na saka ran zasu tashi, haka na haƙura saboda jin zan rasa sallah. Koda na idarma na sake gwada tashinsu amma basu tashinba, nanma haka na haƙura, sai dai zuciyata na mamakin irin wannan nauyin barci haka?, nima ban fargaba barcin ya kwasheni a wajen.
★★★★★★
A daren ranar yaran jazuga suka dawo gidan da taimakon ƴan sandan nan, duk wani makami da sukasan sun ajiye gidan harda wanda Bilkisu ta gani da yawa a kwali randa ta kasa masa shara duk suka fitar dasu, kayan shaye-shayensu da duk abinda za'a iya kalubalantarsu dashi saida suka fitar dashi. Hakama innar Firdausi sun fito da ita, asibiti suka kaita inda baba yake cikin wani yanayi da baki bai iya musaltawa. Innar Firdausi ta fashe da sabon kuka saboda ganin halin ruɗani da mijinta ke a ciki, gefe yaran Jazuga sukaja baba da inna, suka shinfiɗa musu dokoki tare da gargaɗi mai tsoratarwa. A tsorace baba da inna suka amince kodan son tsira da ransu. Alhaji Lado yace, "Zamu baku ƴarku mu canjata da gawa, munaso kuyi nesa da garinanma gaba ɗaya, koda sau ɗaya naga masu kama daku na rantse saikun mutu dukanku, bayan na gama gallaza muku azaba mara musaltuwa, sannan koda wasa kuka taimaki yarinyar data kashemin ɗa wlhy kuma saikun mutu, dan daga yanzu dukkan motsinku zai cigaba da gudana ne a kan idona". Cikin kuka baba da inna suka amsa. A munafurce aka fiddo firdausi da taimakon likita da shima aka toshe bakinsa da kuɗi, tare da yaran Jazuga da ƴansandan nan. A wata mota aka sakasu harda Firdausi da har yanzuma bata farfadoba, sai dai raunikan jikinta duk sun sami kulawa. A wannan tsohon daren aka nufi asalin ƙauyen su baban Firdausi dasu, sunaji suna gani, suna kuka da ɗunbin tausayin Bilkisu da tunanin tana cikin wane haline? Wane kuma hali zata iya shiga daga nan zuwa safiyar gobe.............✍🏻
https://www.youtube.com/channel/UCl9IGLUXrqUtta-Tjmhoo7Q
*_MANHA HAUSA NOVEL'S_*
_Maza garzaya domin bada gudunmawarka kaima, dan ALLAH a danna mana subscribing, tare da bibiyar shirye-shiryanmu masu ƙayatarwa a koda yaushe, harma da tsaftatattun littatafan hausa masu ƙayatarwa da zasu dinga zuwa muku a Audio, yanzu haka ƘARAYAR ARZEEƘI ya fara sauka, garzaya kar ayi babu ku😉🥰🥰🤝🏻._
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_* ALLAH ka gafartama iyayenmu.😭🙏🏻🏻*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*______________________________________* *_BOOK ONE_* _Shafi na goma sha biyu_ *______________________________________*
............Tun a farkawar da nai a wannan barcin safe da yay nasarar saceni na fahimci lallai ƙaddarar rayuwa ta sake jefoni wani rukunin ajin karatun, dan kuwa babu tantama gidan nan na karuwaine. Wasu hawaye masu ɗumi suka gangaro saman kumatuna, ban damu da sharewa ba na barsu suna cigaba da kwarara tamkar an buɗe fanfo..... "Baƙuwarmu kina ganin kuwa kukan nan bai isa hakaba?". Ɗaya daga cikin waɗanda suka taimakeni ta faɗa tana janye hannun da nai tagumi dashi. Idanu na ɗago na kalleta, ƙyaƙyƙyawace, sannan yarinya shakaf da shekarunta bazasu gaza kamar nawa ba, banbancina da ita kawai jikinta a murje yake alamar akwai jin daɗi tattare da ita, na sauke ajiyar zuciya ina kauda idanuna daga gareta ba tare da na ce uffanba. Ɗayar data shigoce ta katsemu da faɗin, "Sweet gafa Laran gabas can nayi dake akan wasan jiya". Ƴar daɓas ta kwashe da dariya tana zama a bakin katifar, "Bar shegiya kinji Sweet, itadai ai bariki iyawace, kowa kaga yazama wane ya iya allonsa ne, idan ta isa itama ta iya wanke nata". "Kamar kuwa kin shiga zuciyata Sweet, dan nima haka nace mata". Kusan a tare suka taɓe baki, Nazy ta juyo indomie daga cikin tukunya tana ajiyewa gabana, "Sorry bakuwarmu mun barki da yunwa, kinga abincinki nan tun ɗazun tsumayen tashinki mukeyi, kinfa sha barci, saikace wadda bata samun isashen barci daga inda ta fito?". Murmushin yake kawai na mata, sai dai ban iya cemata komaiba itama. Ƴar daɓas tace, "Nikam badan jiya kinyi magana ba da nace kodai ke kurmace, ki daure ki amsa mana tambayoyinmu kafin Uwargida ta shigo gidan nan, dan in bata fara samun wani bayani daga garemu ba zamu fuskanci matsalane akan kawoki, kodai kema rayuwace ta nuna miki hanyar zaɓar ƴancin kankine?". "Neman ƴancin kai kuma?". Cikin tsagwaron mamakin daya mamaye fuskata nake jefa musu tambayar tawa. A tare suka ɗagamin kai, Nazy ta washe haƙora tana cewa, "Ai duk macen da kika gani a gidan nan tazone domin samun ƴancin kanta, sai dai kisamu banbancin dalilan da suka nuna mana hanyar hakance nasararmu". "Wata sabuwa kenan". na faɗa a fili batare dana saniba. Atare suka maimaita abinda na faɗa ɗin, suka ɗora da faɗin, "Miyasa kikace haka? Kina ganin hanyar da muke bata dace da tsarinkiba kika fito da ga gidanku?". Murmushi nayi ina lumshe ido, wasu hawaye suka sake ziraromin, hannu na saka na sharesu a karo na farko, na kallesu sosai cikin matuƙar tausayawa kanmu, "Ni ba wannan harkar nazo yiba, ƙaddarar rayuwace kawai ta kawoni cikin taku ƙaddarar". Shiru duk sukayi suna kallona, nima ban sake cewa komaiba na zame na kwanta ina cigaba da kukana, tsawon loakaci muna a haka babu wanda ya sake cewa komai, sai zuwa can ƴar daɓas tace, "To ki daure ki tashi kici abincin, sannan idan bamu shiga rayuwarkiba dan ALLAH ki bamu labarinki". Shiru ban motsaba, bankuma iya cewa da ita komaiba, babu abinda ke sukar zuciyata sai halin dana bar ƴar uwata Firdausi a ciki tare dasu Inna, saiko kisan Jazuga danai da hannuna, na ɗago hannuna ina kallo, wasu sabbin hawayen suka sake ziraromin, jinake inama ni Jazuga ya kashe, dana huta, koba komai zan kusantu da iyayena, na rushe da kuka mai sauti ba tare da nasan muryata tayi ƙarfi irin hakanba. Akusan tare sukai kaina suna tambayata lafiya?, yanzunma dai basu iya samun amsaba daga gareni har wata mata ta shigo. Barina sukai duk suka juya gareta, cikin matukar ladabi da girmamawa suka shiga gaishe ta. Amsawa take a dake, yayinda idanunta ke a kaina ko kyaftawa batayi, batare data ce musu komaiba ta nunani da ɗan yatsa. Nazy ce tai saurin faɗin, "Uwargida baƙuwace da jiya muka taimaka a ƙofar gidan wasa, Babu ne kuma ya bamu ƙwarin gwiwar hakan, yakuma sanar mana zai faɗa miki da safe". Shiru bata amsa ma Nazy ba, sai takowa da tayi zuwa gabana, da hannunta taimin alamun na miƙe zaune, babu musu na tashi danni tsoro ma ta bani, gata garjejiya da tsaho da ƙiba, kaina a ƙasa murya na rawa nace, "Ina kwana?". Karon farko naji muryarta ta amsa mini, sai dai kallon ƙurullar da takemin ne ya sakani jin na takura. "Ya sunanki? Mikuma ya kawoki nan?". Shiru kamar bazance komaiba, wani wanda bansan dashiba ya daka min tsawa, hannu ta ɗaga masa alamar ya bari, niko da naketa rawar jiki sai ta tsugunna gabana tana cemin, "Kinga nutsu faɗamin". Tamkar zan haɗiyi zuciyata na mutu dan tsoro nace, "Sunana Bilkisu, ƙaddarar rayuwace kuma ta kawoni nan ɗin". Batace komaiba ta cigaba da kallona tsawon sakwanni, sai kuma ta miƙe tana faɗin, "Ƴar daɓas ku bata dukkan kulawa, tana bukatar hutu koda na kwana uku ne, amma zuwa dare kuzo da ita gidan wasa". Da to suka amsa mata cike da ladabi, itako ta fice tana ƙara jin kanta sama.
Tun daga hakan babu wanda ya sake tambayata komai har dare, sune suka sani yin wanka tare da bani kayan sakawa, amma ganin wando da rigane nace musu bana sakawa su bani zani, Har Nazy zatai musu, sai ƴar daɓas ta hanata, siket da riga na wani yadi mai ƙyau suka bani, ba musu na amsa na saka, danni burina daga wannan fitar bazan sake dawowa ba. Kusan ƙarfe goma na dare muka fita, tsakanin gidan wasan nasu dana kwanta a ƙofar jiya da gidan babu wani nisa, duk wanda yazo saiya saka kuɗi yake shiga, amma mu sai aka barmu muka shige bayan kawai su Nazy sun saka sunansu a wani littafi. Ƙaton wajene da aka jerama kujeru tamkar aji ko gidan kallon wasan ball, sai ko dima-ɗiman sifiku na kiɗa, ƴammatane bila adadin cikin shiga mai tada hankalin duk wani mai aƙidar tarbiyya, sai maza dake ƙalilan a wajen, Muma wajen zaman muka samu muka zauna, ni dai sai baza ido nake ina kallon ikon ALLAH. bamufi zaman mintuna talatinba wasa yafara gudana, ni dai sam bammaga abin birgewa a wajenba, amma su sai ihu da sowa sukeyi, wasu suna fita suna liƙa kuɗi. Abinda yafi bani mamaki shine yanda manyan mata ƴan gayu keta shigowa ɗai-ɗai wajen suna ɗaukar ƴammata, suna fita. "Mikenan?" Na faɗa a zuciya ba tare da nasan maganar ta fito fili ba. Nazy dake gefena tace, "Akanmi kike magana Balki?". Kallonta nai da tabbacin maganata ta fito fili kenan, banyi nauyin bakiba nace, "Akan waɗanda naga ana ɗauka ɗai-ɗai ana fita dasu nake magana". Murmushi Nazy tayi ta ɗauke kanta tamkar bazata amsa minba, kusan mintuna uku harna fidda ran hakan sai naji tace, "Duk wanda kikaga an fita da ita tayi kasuwane, a tsarin gidan wasannan yaune ranar baje kolin haja, wasu daga wannan ɗaukar da za'ai musu sun tafi kenan, dan kuwa sunzama hajiyoyi na gaske masu ƙazaman kuɗi, duk wata hajiya dakikaga ta shigo nan mai ɗunbin dukiyace, acikin abinda zata jiƙaki dashi idan ta ɗaukeki bazai tsunkuli koda kashi ɗaya a cikin goma na dukiyartaba......." Maganarta ta katse sakamakon zuwan wata hamshaƙiyar hajiya wajen namu, yanda ta kafeni da ido tamkar wata mayyane ya sani jin faɗuwar gaba, saurin fara karanto "Hazbinallahu wa ni'imal wakil" nayi ina janye idona daga shashensu. Batace komaiba tai murmushi tana maida kallonta ga ƴar daɓas da tun ɗazun na lura ranta a jagule yake, dan sam bata da walwala ko sukuni, duk wadda tazo kuma inda muke saita ɓata fuska. Murya a yangance hajiyar ke faɗin, "ƴar daɓas wannan karonma bazaki sallama minba? Na ƙara ruɓanya kuɗin wancan karon sau biyu, harma da ƙyautar mota". Shiru ƴar daɓas bata ɗagoba, bakuma tace komaiba, Murmushi naga Nazy tayi tana matsawa jikin ƴar daɓas ɗin sosai, ta ɗago tana kallon hajiyar cikin fari da idanu, "Hajjaju sweetyna ba kuɗin kowa bane a gabanta, nikaɗai nasan yanda nake sarrafa kayata har take ganin babu mai iya matan sai ni, kibar ƙwaƙwa da wahal da kanki a kan kowaccenmu, ɗakin wasannan cike yake da ƴammata masu aji kuma kyawawa, kizaɓi duk wadda tai miki zaki samu da taimakonmu, dan zamu shige miki gaba wajen Uwargida". Ajiyar zuciya Hajiyar taɗan sauke tana sake maida kallonta gareni, ina kallonta taima Nazy nuni dani cikin wani salo. Dariya Nazy tayi, har ƴar daɓas ta ɗago tana kallonta, nima dai kallonta nayi, taimin kallo ɗaya tana ɗauke kanta da faɗin, "Hajjaju mutan makka, banƙi zaɓinki ba, sai dai fa wannan *ƙwai cikin ƙaya* ce, sabuwar hajace da batasan kasuwar da take cikiba, tana buƙatar lokaci kafin a buɗeta Uwargida ta saka cinikinta bayan tamata sabis, kinsan duk abinda Uwargida bata ɗanɗanaba baya shiga a hajar saidawa". Wani shegen ƙayataccen murmushi hajiyan tayi, ta ɗaga yatsunta uku da sukasha gwala gwalai tana kaɗawa, "Zan zauna da Uwargida, sannan ku na hannun damartane, inaso ku tayani barbaza manufofi, dan inason samun sabuwa dal a leda wannan karon, a ɗaki zan sakata dindin saboda tsaro, idan har nasamu wannan hajar naimuku alƙawarin kuɗade masu nauyi da ƙyautar mota, tareda kaiku duk ƙasar da kuke buƙata Honeymoon". "Zamu gwada, ki bamu kwanaki bakwai kacal". Nanma murmushi tayi, ta zaro kuɗi masu yawa a bag ɗinta tabasu. Sagadada nai da baki ina kallonsu, danni sam ban fahimci dukkan zaurencensu ba, jin an kamo hannuna sai nai firgigit na dawo hankalina, hajiyarce dai, bangama dai-daitaba ta kuma tsunbula tunanina a ruɗani, dan kuwa hannuna ta sumbata tare da kashemin ido ɗaya cikin wani irin salo". Ko motsi kasayi nayi, na bita da kallo harta fice riƙe da hannun wata yarinya.
Dariyar su ƴar daɓas ce ta sani maida kallona garesu, Nazy tace, "Ƴar daɓas da alama fa Balki hajiya ta fara kaita network, irin wannan suman zaune haka". Dariya suka sake kwashewa dashi suna taɓawa. "Dan ALLAH kumin bayani mana?". Cikin dariya ƴar daɓas tace, "bakya bukatarsa a yanzu Balkisu, ki kwantar da hankalinki zaki fahimci komai, mudai fatanmu ki riƙe wannan harkar, dan harkace mai cike da ƴanci, babu ruwanki da wulaƙancin wani banza shi namiji, jinsin dake kallonki a ƙasƙance, ya aureki ya kaiki gidansa yana wulaƙantawa, bakida wani muhimmanci saina haifa masa ƴaƴa da gadin gida, wannan kuwa gashin kanki zakici, sai kinso wata ta saka miki zoben mallaka ma". Nikam sunma ƙara ruɗar dani, hakan yasa nai shiru ban sake tambayaba. Muna nan zaune sai da gidan kusan kashi biyu bisa ukun mutanen gidan suka fice, tsurarun mazan wajenma sun ɗauki ƴammata sun fice, muma tashi mukai muka fito domin komawa gida........
_______________________ JAWAAD _______________________
...............A yau Jawaad bai koma gidaba, bai kuma nema Shahudah ba, dan tun fitowarsa ya fahimci bata kwana a sashen nasuba, hakan ba wani sabon abu bane a wajensa, dan abu kaɗanne zai haɗasu taje takai ƙararshi. A wannan daren suka tsara abubuwa masu yawa shi da su Hafeez Umar akan kubutar da Alhaji Sadi kokino (ba giyar yaroba), yanda tsarin nasu yazo komai ya gamsar dasu, dan haka suka kwanta cike da farinciki bayan sun gamawa Jawaad tsiya akan yatashi ya tafi wajen matarsa. Murmushi kawai yayi, danshi mutumne mai yawan zurfin ciki, bai yarda kowa yasan matsalar gidansaba komai kusancinsa da kai, shiyyasa ko kararsa Shahudah ta kai, idan aka kirasa abinda kawai suke iyaji daga bakinsa shine (ba komai), har ƙannen mahaifiyarsa su Umma bai taɓa zama ya sanar musu matsalar Shahudah ba, sai dai ƴan gidan su Jawaad su kawo musu gulmar. Jabeer dake gefensa yace, "Boss mufa da gaske mukeyi bazaka kwanar mana ananba, kaje wajen amarya taimaka tausar gajiyar da ka sha yau, mun yafe mata". Harara Jawaad ya watsa masa, yaja filo yana kwanciya saman Sofar dake cikin ɗakin tare da zungurin Jabeer da kafa, tashi Jabeer yay a kusa dashi yana dariya da riƙe gefen ƙugunsa da Jawaad ya shura. Cikin danne abinda ke sukar ransa yace, "Waini korata kukeyine? To babu inda zanje, itace ai tace muyi hirar yaushe gamo". Carab Aliyu ya amshe da cewa, "A lallai Shahudah, amaryar tamu mai haƙurice wlhy, mun kwa gode mata, kuma tunda mun fito sai an sake mana sabon biki da bamu ganiba". Duk dariya sukayi banda Jawaad daya ɗauke kansa tamkar baisan sunayi dashi bane..... "Alhaji kayi shiru?" cewar Jabeer yana zungurinsa da biron hannunsa da suka gama rubuce-rubuce". Baki Jawaad yaɗan tabe, sai kuma ya tashi zaune yana faɗin, "Kunga kubar wannan shirmen malamai, ya kamata gobe fa kowa yaje yaga iyalansa koda a ɓoyene, kafin komai ya dai-daita". Dukansu kallonsa suke da murmushi a fuskarsu, ƙaunarsa na sake shiga musu rai, Aliyu yay karfin halin amsa masa, "Amma kana ganin babu damuwa Jay? Da kawai an haƙura munbi dukkan sharadin nasu yanda suka faɗa". Ajiyar zuciya Jawaad yayi, yace, "Aliy dokarsu ni bata wani dameniba, kawai abinda ya cancanta nake dubawa". Kansu duk suka jinjina masa saboda gamsuwa da maganarsa, Hafeez ya miƙe tsaye ya dawo kusa dasu, sai da ya zauna yana kallonsu kafin yace, "Anya kuwa Jay kana ganin mahaifin Surayya zai bani damar ganinta ita da Suhail?". Shiru sukai su duka, kusan sakwan goma Jawaad ya ɗago kansa, guntun murmushi yayi yana dafa kafaɗar Hafeez ɗin, "Karka damu Broth, namaka alƙawarin zan kawo maka Surayya har gidannan itada Suhail, kuma Aliyu da Jabeer hakan inaga ya dace muyi". Bai jira amsarsu ba ya tashi ya shige bayin dake cikin ɗakin, duk binsa sukai da kallo a wani irin yanayi mai wahalar fassara.
★★★★★★★
Kamar yanda yay alƙawari washe gari da safe sai da ya cika, dan kuwa duk sai gashi da matansu da ƴayansu, Aliyu ne kawai matarsa bata haihuba, dan aurensu da wata uku abin ya faru, Jabeer kam da yarinyarsa ɗaya Fatima, sai cikin daya barta dashi ta haifi namiji aka saka masa sunansa. Hafeez kuma yaronsa ɗaya Suhail. Sunyi murna sosai da ganin juna, hartakai saida Jawaad yay musu hawaye, zare jikinsa yay shima ya nufi gida wajen nasa iyalin dukda yasan ba lallai ya tarar da abu mai daɗiba.